Shugaba Tinubu Ya Tabo Batun Biyan 'Yan Bindiga Kudin Fansa
- Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ce gwamnatin tarayya ba za ta biya masu garkuwa da mutane kuɗin fansa ba
- Ya bayyana cewa gwamnati za ta ɗauki sababbin matakan yaƙi da ta’addanci da sauran ayyukan ta’addanci a faɗin ƙasar
- Shugaba Tinubu ya ce za a ƙara yawan rundunonin sojoji daga takwas zuwa 12 domin inganta saurin kai ɗauki
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
FCT, Abuja - Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ce gwamnatinsa ba za ta biya ’yan ta’adda kuɗin fansa ba.
Shugaba Tinubu ya bayyana cewa za a ɗauki matakan dabaru domin murƙushe masu aikata laifuffuka a faɗin Najeriya.

Source: Facebook
Tinubu ya bayyana hakan ne ranar Alhamis, 30 ga watan Yulin 2026 yayin da yake karɓar Olubadan na Ibadanland da mambobin Majalisar Olubadan a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, kamar yadda Dada Olusegun ya sanya a shafinsa na X.
Shugaba Tinubu ya yabawa jami'an tsaro
Shugaban ƙasar ya yabawa jami’an tsaro kan nasarar aikin ceto da aka gudanar a jihar Oyo, yana mai cewa matsalolin tsaro sun sa gwamnati ci gaba da nazari tare da sake duba tsare-tsarenta da ayyukanta.
“Ina taya ku murnar nasarar aikin ceton da aka yi a jihar Oyo. Ina ganin mun samu nasarar ne saboda goyon bayanku da addu’o’inku. Na yarda da ku cewa ya kamata mu yabawa maza da mata na rundunar sojoji kan kyakkyawan aikin da suka yi."
“A madadinsu, na karɓi saƙonku, kuma zan isar musu da wannan saƙo.”
- Shugaba Bola Tinubu
Darussan da ake koya
Tinubu ya ce duk wani lamari da ya shafi tsaro yana bai wa gwamnati damar koyon sababbin darussa domin inganta tsarin tsaron ƙasar.
Shugaban ƙasar ya ce gwamnati ta ɗauki sabuwar hanya wajen yaƙi da ta’addanci da garkuwa da mutane, yana mai jaddada cewa biyan kuɗin fansa ba zai kasance cikin dabarunta ba.
“Kuma kun ga cewa za mu ba su amsa ta fuskar yanki da adadi kan ƙalubalen. Mun ƙi biyan kuɗin fansa; mun san yanayin dazuzzuka, kuma muna da mafita kan matsalar.”
- Shugaba Bola Tinubu

Source: Twitter
Za a ƙara rundunonin sojoji
Tinubu ya bayyana cewa ana ƙara yawan rundunonin sojojin Najeriya daga takwas zuwa 12 domin rage lokacin kai ɗauki da kuma ƙarfafa yaƙi da ta’addanci.
“Kun ga cewa daga rundunoni takwas, yanzu muna ƙara su zuwa 12 domin rage lokacin kai ɗauki, tare da bai wa wannan martani ƙarfin da ake buƙata domin mu kayar da ta’addanci. Wannan abu ne mai matuƙar muhimmanci, kuma muna aiwatar da shi.”
- Shugaba Bola Tinubu
'Yan bindiga sun sace dalibai a Ogun
A wani labarin kuma, kun ji cewa 'yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun sace ɗalibai takwas na Gateway ICT Polytechnic, Saapade (GAPOSA).
'Yan bindigan sun sace daliban ne bayan sun kai hari gidan da ɗaliban ke zaune a Ipara, ƙaramar hukumar Remo ta Arewa ta jihar Ogun.
Asali: Legit.ng

