Manyan Labarai A Yau
Wasu 'yan bindiga dauke da makamai sun yi awon gaba da matafiya a jihar Plateau. Tsagerun 'yan bindigan sun sace mutanen ne da ke kan hanyar zuwa Maulidi.
Wasu 'yan majalisu fuskanci barazanar kiranye daga wajen mutanen da suke wakilta. Kiranyen dai na zuwa ne sakamakon rashin gamsuwa da wakilcin da suke yi.
Amurka ta bayyana cewa ba za ta tura sojoji zuwa Najeriya ba, tana mai cewa sanya kasar cikin jerin CPC hanya ce ta diflomasiyya don karfafa gyare-gyare.
Gwamnatin tarayya karkashin jagorancin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ta sanar da lokacin da sababbin jakadu za su fara aikin wakiltar Najeriya a kasashen waje.
Wata kungiya mai suna Tinubu Vanguard ta janye goyon bayanta ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu. Kungiyar ta bayyana cewa an yi watsi da al'amuranta.
Attajiri lamba daya a Afirka kuma shugaban Dangote Group, Alhaji Aliko Dangote ya nemi Kailani Mohammed ya nemi afuwarsa cikin kwanaki bakwai ko su hadu a kotu.
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ba da hutu don bukukuwan Kirsimeti da sabuwar shekara. Gwamnatin ta ayyana ranaku 3 a matsayin lokacin hutu ga 'yan Najeriya.
Shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasa (EFCC), Ola Olukoyede, ya yi zargi kan wasu gwamnoni. Ya zarge su da yin sama da fadi da kudin tsaro.
An samu asarar dukiya mai tarin yawa bayan da gobara ta lakume wata babbar kasuwa a birnin Kano. 'Yan kasuwar sun nemi gwamnati ta kawo musu dauki
Manyan Labarai A Yau
Samu kari