An Dauki Gwamna 1 daga Arewacin Najeriya an ba Shi Lambar Yabo ta ZIK a Kasar Waje

An Dauki Gwamna 1 daga Arewacin Najeriya an ba Shi Lambar Yabo ta ZIK a Kasar Waje

  • An karrama Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara da lambar yabo ta zaman lafiya da kyayyawan shugabanci a kasar Ghana
  • An yabawa gwamnatinsa kan sauye-sauyen tattalin arziki da shugabanci nagari a Zamfara da ke Arewa maso Yamma
  • Gwamnan ya ce lambar yabon za ta kara masa kwarin gwiwar yin aiki domin ceto jihar daga dukkan wani kalubale

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Ghana - Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya samu lambar yabo ta ZIK International Peace and Leadership Award a kasar Ghana.

An karrama Gwamna Lawal da wannan lambar yabo ne saboda nasarorin da gwamnatinsa ta samu cikin shekaru uku da suka gabata.

Dauda Lawal.
Gwamnan jihar Zzmfara lokacin da ya karbi lambar yabo ta ZIK a birnin Accra na kasar Ghana Hoto: Dauda Lawal
Source: Facebook

Daily Trust ta ruwaito cewa an gudanar da bikin bayar da lambar yabon karo na 7 a ranar Juma’a, 7 ga watan Agusta, 2026 a British Council da ke Accra, babban birnin Ghana.

Kara karanta wannan

Annoba mai alaka da kudaje ta barke a Bauchi, mutane sun fara mutuwa

Kwamitin gudanarwa da majalisar kula da lambar yabon ZIK sun ce daga cikin dalilan karrama Gwamna Dauda Lawal akwai gagarumin ci gaba da ya samu a fannin shugabanci da sauye-sauyen tattalin arziki a Jihar Zamfara.

An yabi salon shugabancin Dauda Lawal

Shugaban kwamitin amintattu na ZIK Pan-African Award, Farfesa Echefuna R.G. Onyeabadi, ya bayyana cewa manufar lambar yabon ita ce karrama mutanen da ke bayar da gagarumar gudunmawa wajen yi wa al’umma hidima.

Bayan karbar lambar yabon, Gwamna Dauda Lawal ya nuna godiyarsa, tare da alkawarin kara kaimi wajen ceto da sake gina Jihar Zamfara.

Ya ce:

“Na sadaukar da wannan lambar yabo ga daukacin al’ummar Jihar Zamfara. Gwamnatina ta yi ta kokari tukuru domin tabbatar da cewa jihar za ta iya gogayya da kowace jiha a Najeriya.
"Wannan shi ne alkawarin da muka dauka, kuma cikin shekaru uku kacal mun zarce abin da ake tsammani.”

Gwamna ya bayyana nasarorin Zamfara

Kara karanta wannan

Kano ta sake shiga gaban jihohi, Gwamna Abba ya samu lambar yabo daga NAWOJ

Gwamna Lawal ya ce gwamnatinsa ta sauya fasalin Zamfara ta hanyar ayyukan sabunta birane, tare da gina filin jirgin sama na zamani wanda ba a taba irinsa a jihar ba tsawon shekaru 30 da kafuwarta.

Ya kara da cewa an samu gagarumin ci gaba a fannonin tsaro, gyaran ma’aikatan gwamnati, ilimi, lafiya da sauran bangarori, cewar rahoton Premium Times.

Dauda Lawal.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal a gidan gwamnati da ke Gusau Hoto: Dauda Lawal
Source: Facebook

Ya ce:

“Ina godiya ga masu shirya wannan lacca da lambar yabo ta shekara-shekara. Wannan karramawa tana da matukar muhimmanci a gare ni, kuma za ta kara min kwarin gwiwar yin abubuwa fiye da haka domin al’ummata. Zamfara na kan hanyar ci gaba.”

Za a dauki sababbin malamai a Zamfara

An ji cewa gwamnatin jihar Zamfara ta sanar da cewa ta bude kofar ɗaukar malamai 3,050 domin cike giɓin malamai a makarantun gwamnati.

Kwamitin ɗaukar malaman ne ya sanar da hakan a cikin wata sanarwa da Babbar Sakatariyar Ma'aikatar Ilimi, Kimiyya da Fasaha ta jihar, Maryam Yahaya Shantali, ta sanya wa hannu.

A cewar kwamitin, manufar ɗaukar malaman ita ce ƙarfafa ilimin bai ɗaya ta hanyar tura ƙwararrun malamai zuwa makarantun da ke karkara da sauran wuraren da ake fama da ƙarancin malamai.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262