Shugaba Trump Ya Yi Maganar Lokacin Kawo Karshen Yaki da Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
- Shugaban kasar Amurka, Donald Trump, ya sake tabo batun lokacin kawo karshen yakin da kasarsa ke yi da Iran
- Donald Trump ya bayyana cewa za a iya kawo karshen yakin ta hanyar cimma yarjejeniya ko akasin haka
- Shugaban na Amurka ya kuma nuna cewa nan da kwanaki biyu masu zuwa wani abin ban mamaki zai iya faruwa
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Birnin Washington, Amurka - Shugaban kasar Amurka, Donald Trump, ya sake yin magana kan yakin da kasarsa ke yi da Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Donald Trump ya bayyana cewa yaƙi da ƙasar Iran na iya ƙarewa nan kusa, inda ya shaida wa duniya cewa su zuba ido su ga "wasu kwanaki biyu masu ban mamaki".

Source: Getty Images
Dan jaridar ABC News Jonathan Karl ya ce Trump ya sanar da shi hakan a wani rubutu da ya yi a shafinsa na X.
Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da dakarun Amurka da ke gudanar da toshe hanyoyin ruwa, suka tilastawa jiragen ruwan Iran komawa baya yayin da suke ƙoƙarin barin tashoshin kasar.
Trump a kan kawo karshen yaki da Iran?
Shugaba Trump ya bayyana cewa ba ya tunanin akwai bukatar sake tsawaita yarjejeniyar da aka cimma tsakanin Amurka da Iran.
"Ina jin za ku ga wasu kwanaki biyu masu ban mamaki a gaba. Da gaske nake."
- Donald Trump
Da aka tambaye shi ko yaƙin zai ƙare ne da wata yarjejeniya ko akasin hakan, sai ya kada baki ya ce:
"Zai iya ƙarewa ta kowane ɓangare, amma ina jin yarjejeniya ta fi dacewa domin hakan zai ba su damar sake gina abubuwan da aka lalata."
"Haƙiƙa yanzu suna da gwamnati ta daban. Ko ma dai yaya abin yake, mun riga mun kawar da masu tsattsauran ra'ayi. Sun tafi, ba sa tare da mu yanzu."
"Idan ba ni ne shugaban ƙasa ba, da duniya ta shiga babbar matsala."
- Donald Trump

Source: Facebook
Shirin sabuwar tattaunawa a Islamabad
Jami’ai daga Pakistan, Iran, da wasu ƙasashen yankin Fasha sun tabbatar da cewa tawagogin tattaunawa na Amurka da Iran na iya komawa Islamabad a ƙarshen wannan mako.
Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta bayyana cewa akwai yiwuwar tawagar Pakistan za ta isa Iran a ranar Laraba domin isar da saƙonni daga Washington.
Tattaunawar ƙarshen makon da ya gabata ta ruguje ne ba tare da yarjejeniyar kawo ƙarshen yaƙin da Trump ya ƙaddamar tare da Isra'ila a ranar 28 ga watan Fabrairun 2026 ba.
Shugaban Iran ya magantu kan yaki
A wani labarin kuma, kun ji cewa Shugaban kasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya bayyana cewa kasarsa ba ta da niyyar mika wuya.
Masoud Pezeshkian ya bayyana cewa babu wata babbar kasa a duniya da za ta iya tursasa al’ummar Iran yin biyayya ko mika wuya.
Shugaban na Iran ya nuna cewa babu dalilin da zai sanya a kai hare-hare kan kasarsa domin hakan ya sabawa dokar kasa da kasa.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

