Manyan Labarai A Yau
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kyauta ga sababbin jakadun Najeriya. Shugaban kasar ya gwangwaje su da filaye a babban birnin tarayya Abuja.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya aika da wasika ga majalisar dattawan Najeriya. Shugaban kasar yana neman a amince da nade-naden da ya yi a NHRC.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasara yayin wata arangama da suka yi da 'yan ta'adda a Borno. Sojojin sun kashe 'yan ta'adda yayin artabun da suka yi.
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya yi magana kan nada Murtala Sule Garo a matsayin mataimakinsa. Gwamna Abba ya ce mutum ne mai son kawo ci gaba.
Babbar kotun tarayya mai zama a Abuja ta hana hukumar IKEC amincewa ko shiga tarukan jam'iyyar ADC na jihohi da tsagin Sanata David Mark ya shirya.
'Yan bindiga sun kashe farar hula uku a wani hari da suka kai wa ayarin sojojin Ghana a yankin Binduri, yayin da sojoji suka kashe mahara bakwai.
Gwamnatin Trump na nazarin tayin Iran na bude mashigin Hormuz muddin aka janye takunkumi, amma rashin maganar nukiliya na kawo cikas ga yarjejeniyar.
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya yi zargin cewa wasu yan Najeriya da ba su da kishin kasa ne ke kokarin lalata harkar tsaro don cimma burin siyasa.
Kasar Hadaddiyar Daular Larabawa ta sanar da ficewa daga kungiyar OPEC sakamakon yakin Iran, matakin da ake ganin zai ba kasar damar kara yawan man da take samarwa.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari