Dubu Ta Cika: 'Yan Sanda Sun Cafke Rikakken Jagoran 'Yan Bindiga
- Rundunar 'yan sandan jihar Zamfara ta samu nasarori a yakin da take yi da 'yan bindiga da sauran masu aikata laifuffuka
- Jami'an rundunar 'yan sandan sun samu nasarar cafke wani tantirin jagoran 'yan bindiga a karamar hukumar Kaura Namoda
- Hakazalika, jami'an 'yan sandan sun samu nasarar cafke wasu mutane da ake zargi da laifin gudanar da sana'ar sayar da ganyen tabar wiwi
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Zamfara - Rundunar 'yan sandan jihar Zamfara ta bayyana cewa ta samu gagarumar nasara a yaƙin da take yi da 'yan bindiga da manyan laifuffuka.
Rundunar 'yan sandan ta bayyana cewa ta cafke wani da ake zargi jagoran 'yan bindiga ne tare da ƙwato makamai, miyagun ƙwayoyi, da kuma kayayyakin sata a faɗin jihar.

Source: Twitter
Jaridar Leadership ta ce jami’in yaɗa labarai na rundunar, DSP Yazid Abubakar, ya bayyana hakan yayin da yake jawabi ga manema labarai a ranar Laraba, 29 ga watan Afirilun 2026.
'Yan sanda sun cafke jagoran 'yan bindiga
Kakakin 'yan sandan ya ce an samu waɗannan nasarori ne tsakanin mako guda da kwamishinan 'yan sandan jihar, Ahmad Muhammad Bello, ya kama aiki.
Ya lura cewa waɗannan ayyuka wani ɓangare ne na sabon ƙoƙari na dawo da tsaro da kuma kare rayuka da dukiyoyi a cikin jihar, rahoton Radio Nigeria Kaduna ya tabbatar da hakan.
Rundunar ta sanar da kama wani da ake zargi jagoran 'yan bindiga ne, Audu Maikano, yayin wani samame na haɗin gwiwa tsakanin jami’an tsaro a ƙauyen Dan-Makulu, da ke ƙaramar hukumar Kaura Namoda.
“Jami’an ƴan sanda ne suka gudanar da aikin tare da haɗin gwiwar sojoji, biyo bayan sahihan bayanan sirri kan ayyukan wata ƙungiya da ke addabar mazauna yankin, musamman a kan hanyoyin da suka haɗa Kaura Namoda da Kasuwar Daji."
“Abubuwan da aka ƙwato daga hannun wanda ake zargin sun haɗa da bindiga kirar AK-47 da aka ƙera da hannu, alburusai, bindigun gargajiya, adduna, layu, da wayoyin hannu da dama."
"Ƴan sanda na ci gaba da bincike don kamo sauran mambobin ƙungiyar."
- DSP Yazid Abubakar
An kama masu sayar da wiwi
Jami’in yaɗa labaran ya bayyana cewa a wani samame na daban, an kama mutane biyu a Gusau bisa zargin mallakar ganyen da ake zargin tabar wiwi ne.
An bayar da rahoton cewa waɗanda ake zargin sun amsa laifin gudanar da sana’ar sayar da ganyen.
Bugu da ƙari, ƴan sanda sun kai samame wata maboyar masu shan ƙwayoyi a yankin Gangaren Gulbi, inda suka ƙwato kwalaben kodin, hodar roba da sauran abubuwan da suka shafi shaye-shaye.

Source: Original
An cafke masu ganganci da babura
Rundunar ta kuma tabbatar da kama wasu mutane uku da ke da alaƙa da ayyukan ƙungiyar “Yan Arlit”, waɗanda aka sani da guje-guje da babura ba tare da kiyayewa ba da kuma tayar da hankalin jama’a.
An ƙwato abubuwa da suka haɗa da ganyen da ake zargin wiwi ne, bututun shakar ƙwayoyi, wuƙa, da babura da dama.
Rundunar ta jaddada cewa ana ci gaba da gudanar da ayyuka domin kamo sauran mambobin ƙungiyar da suka tsere.
'Yan bindiga sun kashe fasto
A wani labarin kuma, kun ji cewa 'yan bindiga sun kai hari wurin wani taron wa'azi inda suka hallaka fasto tare da sace mutane da dama a jihar Ekiti.
Maharan sun mamaye filin taron ne a lokacin da ake tsaka da gudanar da wa’azi, inda suka bude wuta kan mai uwa da wabi.
Majiyoyi sun bayyana cewa miyagun maharan sun zo ne a ayari kuma suna dauke da mugayen makamai.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng


