Manyan Labarai A Yau
Wata fitacciyar jarumar fim a Najeriya, Doris Ogala ta bayyana cewa da alamu ba za ta yi tsawon rai ba aaboda abin da Fasto Okafor ya mata na yaudara a soyayya.
Babbar kotun jihar Rivers mai zama a Fatakwal ta umarci babban alkalin jihar da kada ya karbi takarda ko bin umarnin Majalisa game da tsige Gwamna Siminalayi Fubara.
Fitaccen malamin addinin kirista a Najeriya, Bishop Isaac Idahosa ya yaba waGwamna Umaru Bago saboda matakan da yake dauka na kawar damatsalar taaro a Neja.
Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya tashi daga Abuja zuwa Guinea-Conakry domin wakiltar Bola Ahmed Tinubu a bikin rantsar da Mamadi Doumbouya.
Gwamnatin jihar Sokoto ta fito ta yi martani kan rahotannin da aka yada cewa 'yan bindiga sun farmaki mutane da matsugunansu. Ta ce ba kamshin gaskiya a batun.
Gwamnan jihar Bayelsa, Douye Diri ya aika da sakon gargadi ga sarakunan gargajiya. Gwamna Diri ya gargade su kan ba Fulani makiyaya fili a jihar.
Jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya ta taso tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar a gaba bayan dansa ya zabi marawa Bola Ahmed Tinubu baya.
Gwamnan jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya yi magana kan harin 'yan bindiga a Kasuwan Daji. Ya bayyana dalilin da ya sa suka kai mummunan harin.
Tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya, Atiku Abubakar, ya fitp ya yo martani bayan dansa ya zabi ya goyi bayan tazarcen Bola Tinubu a zaben 2027.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari