Manyan Labarai A Yau
Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, ya yi magana kan makomar jam'iyyar PDP a zaben shekarar 2027. Ya ce masu sukar jam'iyyar za su sha mamaki a zaben 2027.
Shugabar kungiyar ALGON ta jihar Kano, Hajiya Sa'adatu Soj, ta yi murabus daga jam'iyyar NNPP. Ta bayyana dalilin da ya sanya ta dauki wannan matakin.
Shugaban jam'iyyar APC na jihar Kano, Abdullahi Abbas, ya yi magana kan batun ba Gwamna Abba Kabir Yusuf tikitin takara kai tsaye a zaben shekarar 2027.
Kwamitin bangaren marasa rinjaye a Majalisar wakilai ya tabbatar da cewa an yi kari a sababbin dokokin haraji da majalisa ta amince da su, ta fadi wasu daga ciki.
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da murabus dinsa daga jam'iyyar NNPP. Gwamnan ya fice daga jam'iyyar ne a ranar Juma'a, 23 ga watan Janairun 2026.
'Yan bindiga dauke da makamai sun kai harin ta'addanci a jihar Katsina. Tsagerun 'yan bindigan sun kashe jami'an tsaro na 'yan sa-kai a wani artabu.
Rahotanni sun nuna cewa zuwa karfe 1:00 na rana, babu wata wutar lantarki da aka turawa duka kamfanonin raba wutar lantarkin Najeriya, tushen wuta ya dawo 0.
Tsohon mai ba jam'iyyar PDP shawara kan harkokin shari'a na kasa, Emmanuel Enoidem, ya sasanta rikicinsa da Godswill Akpabio. Ya sauya sheka zuwa APC.
Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya nuna damuwa kan yadda ake yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya. El-Rufai ya ce ana mulki ba tare da ka'ida ba.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari