Ragunan Layya Sun Yi Tashin Gwauron Zabi Ana Shirin Babbar Sallah a Jihar Kaduna

Ragunan Layya Sun Yi Tashin Gwauron Zabi Ana Shirin Babbar Sallah a Jihar Kaduna

  • Farashin raguna ya yi tashin gwauron zabi a wsu kasuwannin jihar Kaduna kafin yayin da musulmi ke shirye-shiryen sallar layya
  • Bincike ya nuna cewa farashin dan matsakaicin rago da bai kai girma sosai ba ya tashi daga N150,000 zuwa N250,000
  • Masu saye da dillalai sun danganta tashin farashin da matsin tattalin arziki da matsalar tsaron da ake fama da su a sassan kasar nan

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kaduna, Nigeria - Yayin da al’ummar Musulmi ke shirin bukuwan sallar layya (Eid-el-Kabir), farashin raguna ya yi tashin gwauron zabi a jihar Kaduna.

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya sa mutane da dama sun dakatar da sayen dabbar da za su yi layya da ita duk da wadatar dabbobin a kasuwanni.

Ragunan layya.
Ragunan layya a wata kasuwar dabbobi a Najeriya Hoto: Bello Ado Muhammed
Source: Facebook

Binciken da Vanguard ta gudanar a wasu manyan kasuwannin dabbobi da ke cikin birnin Kaduna ya nuna cewa kasuwannin sun cika da raguna, amma babu masu saye.

Kara karanta wannan

"Yara na 3 sun mutu," Magidanci ya sabawa bayanin sojoji kan kuskuren jefa bam a Neja

A kasuwannin Zango, Rigasa da Bashama Road, ana sayar da kananan raguna tsakanin N150,000 zuwa N250,000, yayin da matsakaita da manyan raguna ke kaiwa daga N300,000 har zuwa Naira miliyan 1, gwargwadon iri da girmansu.

Mazauna Kaduna sun koka

Wasu mazauna jihar Kaduna sun bayyana cewa farashin ya yi tsada sosai idan aka kwatanta da shekarun baya.

Wani magidanci, Abdulrahman Usman, wanda aka gani yana cinikin rago a kasuwar Zango, ya nuna damuwa kan yadda farashin dabbobin ya yi tashin gwauron zabi.

Sai dai ya ce yana fatan farashin zai sauka yayin da ranar Sallah ke kara matsowa.

Wani dillalin dabbobi a kasuwar Rigasa, Alhaji Suleiman Adamu, ya danganta tashin farashin da tsadar sufuri, abincin dabbobi da kuma matsalar tsaro da ke shafar hanyoyin safara.

A cewarsa, karin kudin kula da dabbobin kafin a sayar da su ma ya taimaka wajen tashin farashin, kamar yadda Punch ta kawo.

Wasu raguna sun kai N700,000

Shi ma wani dillali, Bilyaminu Musa, ya ce yana kawo raguna daga jihar Neja domin kwastomominsa na musamman.

“Na shafe kusan shekara 10 ina wannan kasuwanci. Ina kawo raguna ga abokan ciniki na na musamman da suka san darajar irin wadannan raguna,” in ji Musa.

Kara karanta wannan

Jerin gwamnonin Arewa da suka fitar da wadanda za su gaje su a zaben 2027

Ya bayyana cewa daga cikin raguna 40 da ya kawo, an riga an sayar da guda 14.

Kaduna.
Taswirar jihar Kaduna da ke Arewa maso Yammacin Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Da aka tambaye shi farashin mafi karamin da mafi girman rago, ya ce mafi kankanta shi ne ragon N350,000 ne yayin da mafi girma ya kai N700,000.

An ba da hutun babbar sallah a Turkiyya

A wani labarin, kun ji cewa Shugaba Recep Erdoğan ya ba da sanarwar ƙara hutun Sallar Layya na shekarar 2026 zuwa kwanaki tara ga ma'aikatan gwamnati a Turkiyya

Bukukuwan sallar za su fada tsakanin 27 zuwa 30 ga watan Mayu, amma dai yanzu an haɗe su da kwanakin aiki na Litinin da Talata don samun hutu mai tsawo.

Sallar layya, wadda Turkawa ke kira da Kurban Bayram, tana ɗaya daga cikin manyan bukukuwan Musulunci da ake gudanarwa don tunawa da sadaukarwar Annabi Ibrahim (AS).

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262