Manyan Labarai A Yau
Kungiyar NLC ta tabbatar da rasuwar shugaban JNC na jihar Legas, Domingo Michael Adaeleke a taron kwadago na duniya da ke gudana a birnin Geneva.
Tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano, Dr. Nasiru Yusuf Gawuna, na tattaunawa domin komawa jam'iyyar ADC. Nasiru Gawuna na son samun tikitin takara.
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump, ya halarci wasan karshe na gasar NBA. Sai dai, an yi wa shugaban kasar ihu a wajen wasan da aka yi a New York.
Wani jirgin yakin Amurka ya rikito daga sararin samaniya a kusa da mashigar Hormuz. An samu nasarar ceto mutanen da ke cikinsa bayan ya rikito daga sama.
An samu aukuwar hatsarin jirgin kasa a kan hanyar Warri zuwa Itakpe. Hukumar kula da sufurin jiragen kasa ta Najeriya (NRC), ta tabbatar da aukuwar hatsarin.
Tsohon hadimin marigayi Muhammadu Buhari, Bashir Ahmad, ya ba da shawara ga madugun Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya fice daga jam'iyyar NDC.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya rantsar da wadanda za su maye gurbin minitocin wutar lantarki da harkokin kasashen waje a Abuja yau Litinin.
Gwamnatin tarayya ta hannun ma'aikatar kudi ta fara biyan 'yan kwangila na cikin gida basussukan da suka dade suna jira. An biya 'yan kwangila sama da 1,000.
Gwamnatin jihar Borno ta yi martani kan ikirarin cewa an biya 'yan ta'addan Boko Haram kudin fansa kafin kubutar da mutane 360 da aka yi garkuwa da su.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari