Daga zuwa Wurin Taro, Shugaban Kungiyar Kwadago a Najeriya Ya Rasu a Kasar Switzerland

Daga zuwa Wurin Taro, Shugaban Kungiyar Kwadago a Najeriya Ya Rasu a Kasar Switzerland

  • Domingo Michael Adeleke, shugaban kungiyar kwadago t JNC reshen jihar Legas, ya rasu a Geneva bayan gajeruwar rashin lafiya
  • Ya kasance cikin tawagar Najeriya a taron ƙwadago na duniya karo na 114, wanda ke ci gaba da gudana a Geneva da da ke Switzerland
  • Kungiyar NLC ta bayyana rasuwarsa a matsayin babban rashi ga harkar ƙwadago da kare haƙƙin ma’aikata a Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Geneva, Switzerland - Tawagar Najeriya da ke halartar taron kwadago na duniya (ILC) karo na 114 a birnin Geneva na ƙasar Switzerland ta shiga jimami bayan rasuwar fitaccen jagoran ƙwadago, Domingo Michael Adeleke.

Adeleke, wanda shi ne shugaban kungiyar kwadago ta JNC na jihar Legas, ya rasu ne ranar Talata bayan gajeruwar rashin lafiya yayin da yake halartar taron a matsayin ɗaya daga cikin wakilan Najeriya.

Kara karanta wannan

Kwana ya kare: An hallaka mawaki dan asalin Najeriya a Burtaniya

Domingo Michael Adeleke.
Shugaban kungiyar kwadago ta JNC na jihar Legas, Domingo Michael Adeleke Hoto: Mummy Moreni
Source: UGC

Yadda Adeleke ya rasu a Geneva

Rahotannin da Vanguard ta tattaro sun nuna cewa marigayin ya fara fama da rashin lafiya ne a lokacin taron, inda aka garzaya da shi asibiti domin samun kulawar likitoci.

Sai dai duk da ƙoƙarin da aka yi domin ceton rayuwarsa, ya rasu bayan wani ɗan lokaci a asibiti.

Ƙungiyar kwadago ta Najeriya (NLC) ta tabbatar da rasuwar tasa, tana mai bayyana shi a matsayin jajirtaccen ɗan gwagwarmayar kare haƙƙin ma’aikata da walwalarsu.

A cewar wata sanarwa daga jami’in NLC, rasuwar Adeleke babban rashi ne ga ƙungiyoyin ƙwadago a Najeriya.

Gudunmawar Adeleke ga ma’aikata

Marigayin memba ne na kungiyar ma'aikatan gwamnati ta Najeriya (NCSU) kuma ya yi fice wajen fafutukar inganta rayuwar ma’aikata da kare muradunsu.

A matsayinsa na shugaban JNC na Legas, ya taka muhimmiyar rawa wajen tattaunawa da gwamnati kan albashi, walwala da sauran haƙƙoƙin ma’aikata.

Kara karanta wannan

Kwankwaso ya fusata kan rashin tsaro, ya ragargaji Tinubu

NLC ta ce Adeleke ya sadaukar da rayuwarsa wajen tabbatar da adalci, ingantaccen aiki da kuma kare muradun ma’aikata a matakai daban-daban.

NLC ta fara shirin dawo da gawarsa

Shugabannin NLC sun kai ziyara asibitin da aka ajiye gawarsa domin nuna alhini tare da fara shirye-shiryen dawo da gawar zuwa Najeriya.

Kungiyar ta mika ta’aziyya ga iyalansa, abokan aikinsa da kuma daukacin ‘yan ƙwadago a fadin ƙasar nan, kamar yadda PM News ta rahoto.

Yan kwadago.
Wasu daga cikin yan kwadagon Najeriya yayin zanga-zanga kan tsadar rayuwa a Abuja Hoto: NLC Nigeria
Source: Getty Images

NLC ta ce za a ci gaba da tunawa da Adeleke saboda gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban harkokin ƙwadago da kare haƙƙin ma’aikata.

Rasuwarsa ta girgiza mahalarta taron ILC na bana, wanda ya haɗa gwamnatoci, masu daukar ma’aikata da ƙungiyoyin ƙwadago daga sassa daban-daban na duniya domin tattauna batutuwan aiki da walwalar ma’aikata.

Yan kwadago sun taso gwamnatin Najeriya

A wani labarin, kun ji cewa NLC da TUC sun yi barazanar daukar matakai masu tsauri idan ba a dakile yawaitar kashe-kashe, garkuwa da mutane da sauran matsalolin tsaro ba.

Kara karanta wannan

Matsalar tsaro: NLC da TUC sun yi barazanar hana ma'aikata zuwa wurin aiki a Najeriya

Kungiyoyin kwadagon sun ce matsalar tsaro ta kai wani mataki mai hadari, inda ma’aikata a sassa daban-daban na kasar ke fuskantar barazanar rasa rayukansu yayin zuwa aiki.

Shugaban NLC , Joe Ajaero, da Mataimakin shugaban TUC, Oyibo Jimoh, ne suka bayyana hakan a taron yan kwadago na duniya (ILC) da ake yi a birnin Geneva da ke kasar Switzerland.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262