Jirgin Kasa Dauke da Fasinjoji Ya Gamu da Hatsari a Hanyar Warri, Itakpe

Jirgin Kasa Dauke da Fasinjoji Ya Gamu da Hatsari a Hanyar Warri, Itakpe

  • An samu aukuwar hatsarin jirgin kasa dauke da fasinjoji a kan hanyar Warri zuwa Itakpe a ranar Litinin, 8 ga watan Yunin 2027
  • Hatsarin ya jawo asarar wasu daga cikin fasinjojin da ke cikin jirgin bayan da ya goce daga kan layin dogon da yake tafiya a kansa
  • Hukumar kula da sufurin jiragen kasa ta Najeriya (NRC) ta tabbatar da aukuwar lamarin inda ta bayyana cewa an tura jami'an ba da agajin gaggawa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Delta - Wani jirgin kasa dauke da fasinjoji ya gamu da hatsari bayan ya goce daga kan layin dogo a kan hanyar Warri zuwa Itakpe.

Fasinjoji uku ne suka rasa rayukansu biyo bayan gocewar da wani jirgin ƙasa ya yi daga kan layinsa a kan hanyar jiragen ƙasa ta Warri zuwa Itakpe.

An yi hatsarin jirgi a hanyar Warri zuwa Itakpe
Wani jirgin kasa a Najeriya Hoto: @Ogidan_Akinola
Source: Twitter

Tashar Channels tv ta kawo rahoton cewa hatsarin jirgin kasan ya auku ne a ranar Litinin, 8 ga watan Yunin 2026.

Kara karanta wannan

Ndume: Sanata ya faɗi wurin da ya dace Amurka ta kafa sansanin soji a jihar Borno

Hukumar NRC ta yi bayani

Yayin da take tabbatar da aukuwar gocewar jirgin, hukumar kula da sufurin jiragen kasa ta Najeriya (NRC) ta bayyana cewa a halin yanzu sassan jami'an ba da agajin gaggawa da hukumomin da abin ya shafa suna wurin da lamarin ya faru suna duba yanayin da ake ciki tare da samar da taimakon da ya dace.

Shugaban hukumar NRC, Dr. Kayode Opeifa, ya fitar da sanarwar da ke tabbatar da aukuwar hatsarin jirgin kasan a shafin X.

“Hukumar kula da sufurin jiragen kasa ta Najeriya (NRC) tana tabbatar da cewa wani lamari da ya shafi layin jiragen ƙasa na Warri–Itakpe ya auku a yau."
“A halin yanzu jami'an ba da agajin gaggawa da hukumomin da abin ya shafa suna wurin da lamarin ya faru suna duba yanayin tare da samar da taimakon da ya dace."
“Hukumar tana sanya ido sosai kan yadda abubuwa ke gudana, kuma za a fitar da cikakkiyar sanarwa da zaran an samu ƙarin bayanai."

Kara karanta wannan

Babbar magana: An kai harin da ya yi barna mai girma a tsakiyar Israila

- Dr. Kayode Opeifa

Jirgin kasa ya gamu da hatsari a hanyar Warri, Itakpe
Taswirar jihar Delta, tarayyar Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Karanta wasu labaran kan ​jirgin kasa

Hukumar NRC ta dakatar da zirga-zirga

A wani labarin kuma, kun ji cewa an samu aukuwar hatsarin jirgin kasa a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja wanda ya sanya jama'a cikin firgici.

Hukumar kula da sufurin jiragen kasa ta Najeriya (NRC) ta dauki matakin dakatar da zirga-zirgar jiragen kasa a hanyar Abuja-Kaduna har zuwa wani lokaci, sakamakon hatsarin da ya faru.

Hakazalika, shugaban hukumar NRC, Dr. Kayode Opeifa, ya karyata jita-jitar cewa jiragen kasan ba su da inganci, ya kuma ce an fara mayar da kudin tikiti ga dukkan fasinjojin da abin ya shafa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng