Manyan Labarai A Yau
Yan kasuwa sun fara lissafin miliyoyin Naira da suka tafka asarar a wata mummunar gobara da ta auku a kasuwar kayan gida ta Kingsway da ke jihar Kano.
Miliyoyin masu amfani da Facebook da Instagram sun fuskanci matsala bayan dandalin Meta ya samu tangarda da ta shafi shiga da aika sakonni a ranar Juma'a.
Mai magana da yawun bakin gwamnan jihar Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya yi zarge-zarge kan madugun Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, na shirin daukar Rotimi Amaechi a matsayin abokin takararsa a zaben 2027 a inuwar jam'iyyar ADC.
Dakarun sojojin saman Najeriya sun kai hare-hare kan maboyar 'yan ta'adda a jihar Borno. Sojojin sun hallaka 'yan ta'adda da dama tare da manyan kwamandojinsu.
Jagoran jam'iyyar NDC na kasa, Sanata Seriake Dickson , ya nuna cewa ba su karvi ko sisin kwabo ba kafin mika tikitin takara ga Peter Obi da Rabiu Kwankwaso.
Hukumar IAEA ta bayyana yadda aka gudanar da aikin kwashe sinadarin Uranium daga Venezuela zuwa Amurka cikin tsauraran matakan tsaro domin kauce wa barazana.
Gwamnan jihar Katsina, Dr. Dikko Umaru Radda, ya bukaci 'yan bindiga da ke addabar mutane da su zabi hanyar ci gaba maimakon barna domin su rayu.
Hukumar kwallon kafa ta Turai (UEFA) ta zabi Omar Artan, wanda Amurka ta hana shiga kasarta don hura gasar kofin duniya, a matsayin wanda zai hura mata wasa.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari