Manyan Labarai A Yau
'Yan bindiga dauke da makamai sun kai wani harin ta'addanci a jihar Sokoto. 'Yan bindigan sun kashe wani babban limami tare da sace matan aure yayin harin.
Gwamnatin tarayya ta sanar da batun gano wasu ma'adanai masu daraja a duniya a jihar Kaduna, ta ce hakan ya biyo bayan matakan da ta dauka a baya.
Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Ezenwo, ya bayyana rashin jin dadinsa kan gazawar da Najeriya ta yi na samun gurbin zuwa gasar cin kofin duniya.
Sanata mai wakiltar Kebbi ta Kudu a Majalisar Dattawa, Sanata Garba Musa Maidoki, ya yi zargin cewa jam'iyyar APC ta ci amanarsu kan zaben fitar da gwani.
Majalisar dattawa ta yi bakin fuska da aka bai wa sanatoci hudu da suka samu nasara a zaben cike gurbi rantsuwar kama aiki a hukumance ranar Laraba.
Madugun Kwankwasiyya kuma dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam'iyyar NDC, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi barazanar kai Primate Ayodele kotu.
Gwamnatin Sakkwato karkashin jagorancin Gwamma Ahmed Aliyu ta ce ba za ta dauki rahotanni sirri da ke nuna shirin da kasurgumin dan bindiga, Bello Turji ke yi ba.
Ministan tsaron Israila, Israel Katz, ya bayyana cewa ba za su janye dakarun sojojin kasar daga Kudancin Lebanon. Ya ce ko da Amurka ta bukata, ba za su yi ba.
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya nuna damuwarsa kan yadda aka tsaurara sharuddan beli ga tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari