Matasa Za Su Warwasa, An Bude Damar Tallafa wa Mutane 50,000 a Jihohin Najeriya

Matasa Za Su Warwasa, An Bude Damar Tallafa wa Mutane 50,000 a Jihohin Najeriya

  • Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shirin Tinubu Light Initiative domin samar da wutar lantarki mai tsafta ga kananan yan kasuwa miliyan ɗaya
  • Shirin na da burin ƙirƙira tare da sama wa yan Najeriya 50,000 ayyukan yi tare da rage kuɗin gudanar da kasuwanci
  • An kuma ƙaddamar da shirin NextGen Innovation Challenge 2026 domin tallafa wa masu ƙirkire-ƙirkire a Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da Tinubu Light Initiative (TLI), wani shiri na samar da makamashin lantarki mai tsafta a faɗin ƙasa.

Shirin na da nufin Oyebanji samar da wutar lantarki mai araha ga ƙananan, matsakaita da ƙananan masana'antu (MSMEs) akalla miliyan ɗaya.

Tinubu.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu yana rattaba hannu a wasu takardu a Ado Rock, Abuja Hoto: Bayo Onanuga
Source: Facebook

Jaridar Tribune Nigeria ta ruwaito cewa an ƙaddamar da shirin ne tare da NextGen Innovation Challenge 2026, shirin tallafawa mutane masu fasahar kirkire a Abuja.

Kara karanta wannan

Trump ya rattaba hannu kan dokokin da za su kawo cikas ga 'yan Najeriya da wasu kasashe

Ministan Ƙirkire-ƙirkire, Kimiyya da Fasaha, Dakta Kingsley Tochukwu Udeh, wanda Sakatare na Dindindin a ma'aikatar, Dakta Mukhtar Yawale Muhammad, ya wakilta, ne ya jagoranci kaddamar da shirye-shiryen.

Ya bayyana cewa shirye-shiryen za su taimaka wajen mayar da sababbin dabaru zuwa kasuwanci tare da bunƙasa masana'antu ƙarƙashin Ajandar Renewed Hope ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Yadda shirin zai samar da ayyuka 50,000

Muhammad ya ce Tinubu shirin Light Initiative zai samar da makamashi mai araha ga kananan yan kasuwa miliyan ɗaya, rage kuɗin gudanar da kasuwanci, ƙarfafa haɗa mutane cikin harkokin kuɗi da kuma inganta tattalin arziki mai ɗorewa.

A cewarsa, ana sa ran wannan shiri zai samar da ayyukan yi kai tsaye sama da 50,000, ga yan Najeriya tare da rage farashin gudanar da kasuwanci.

A cewarsa:

"Idan muka samar wa 'yan kasuwa makamashi mai tsafta da araha, ba wai muna kunna fitilu kawai ba ne, muna kunna kasuwanci, masana'antu da tattalin arzikin Najeriya."

Kara karanta wannan

Dara ta ci gida: Wani bam ya fashe da ƴan ƙungiyar ISWAP yayin da suke hada shi

NextGen Innovation Challenge ya samu karɓuwa

Darakta Janar na hukumar National Board for Technology Incubation (NBTI), Dakta Kazeem Kolawole Raji, ya ce shirin ya samar da gagarumar nasara tun daga farkon ƙaddamar da shi.

Ya bayyana cewa wani daga cikin mahalarta shirin ya samu alkawarin jarin fam miliyan 1.5, yayin da wasu sababbin fasahohin noma suka fara inganta amfanin gona a jihohin Kaduna da Bauchi.

Minista.
Ministan harkokin kirkire-kirkire, kimiyyya da fasaha na Najeriya, Kingsley Tochukwu Udeh Hoto: @KingsleyUdehSAN
Source: Twitter

Raji ya ce shirin na shekarar 2026 ya samu dubban masu neman shiga daga fannoni daban-daban da suka haɗa da fasahar AI, makamashi mai tsafta, ilimin halittu, lafiya, masana'antu, ilimi, fintech da fasahar sauyin yanayi.

An bude shafin tallafin N50,000 a Najeriya

Rahoto ya zo cewa gwamnatin tarayya ta hannun hukumar SMEDAN ta sake bude shirin ba da tallafin N50,000 ga kananan 'yan kasuwa a Najeriya.

An tsara tallafin ne domin taimaka wa kananan 'yan kasuwa wajen inganta harkokinsu, fadada kasuwanci da kuma samar da karin guraben ayyukan yi.

A cewar SMEDAN, shirin zai kuma taimaka wajen bunkasa harkokin kasuwanci , kara yawan masu sana'o'i da habaka tattalin arziki a matakin kananan hukumomi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262