Manyan Labarai A Yau
Kungiyar SERAP ta dauki matakin shari'a kan gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da hukumar sadarwa ta kasa (NCC) kan karin kudin kira da data.
Gwamnatin jihar Oyo karkashin jagorancin Gwamna Seyi Makinde ta cika alkawarin da ta daukarwa ma'aikata inda ta fara biyan sabon mafi karancin albashi.
An samu asarar rayuka sakamakon fashewar tankar man fetur a jihar Enugu. Gwamnan jihar Enugu ya yi alhini kan hatsarin inda ya yi alkawarin daukar mataki.
Tsofaffin shugabannin kananan hukumomin jihar Osun sun taso Gwamna Ademola Adeleke a gaban kan N183bn. Sun bukaci ya bayyana yadda ya kashe kudaden.
Ana fama da matsalar yunwa a nahiyar Afirika. Da yawa daga cikin kasashen da lamarin ya shafa suna fama da rikice-rikice wanda hakan ya kawo cikas ga aikin noma.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar sheke wani hatsabibin kwamandan 'yan ta'adda. Sojojin sun kuma cafke barayin man fetur tare da ceto wasu mutane.
Miyagun 'yan bindigan da suka kai hari a wani babban asibiti a jihar Katsina, sun bukaci a ba su kudin fansa. Sun nemi a ba su kudin da suka fi rabin miliyan.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun kai harin ta'addanci a jihar Kaduna. 'Yan bindigan sun yi awon gaba da mutane biyar tare da hallaka wani mutum.daya a yayin harin.
Mataimakin shugaban majalisar wakilan Najeriya, Benjamin Kalu, ya yi magana kan cire tallafin man fetur da gwamnati ta yi. Ya ce hakan ya haifar da ci gaba.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari