Manyan Labarai A Yau
Rahotanni a manhajar X da aka yada sun yi ikirarin cewa gwamnatin tarayya ta kara alawus din 'yan NYSC zuwa N77,000 duk wata. An gano gaskiya kan lamarin.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun yi awon gaba da wata tsohuwar kwamishiniya a jihar Delta. 'Yan bindiga sun kutsa har cikin coci sannan suka tafka wannan ta'asar.
'Yan sanda a jihar Bauchi sun yi caraf da hadimin Sanata Ali Ndume da wasu magoya bayansa mutum biyu. Sun cafke su ne bayan sun yi yunkurin yin gangami.
Muhammad Ali Ndume ya ƙi karban sabon ofishin da aka ba shi a majalisar dattawa bayan sauke shi daga matsayin mai tsawatarwa saboda ya soki Bola Tinubu.
Matasa a Najeriya na ci gaba da shirye-shiryen fitowa domin gudanar da zanga-zanga a fadin kasar nan. Zanga-zangar za a yi ta ne saboda tsadar rayuwa da talauci.
Gwamnatin jihar Zamfara karkashin jagorancin Dauda Lawal ta amince da ba da aikin titin hanyar Magami zuwa Dansadau wanda zai lakume makudan kudade har N81bn.
Hukumar sadarwa ta Najeriya (NCC) ta umarci kamfanonin sadarwa da su bude layukan da suka rufe saboda rashin sanya lambar NIN. Ta ja kunnen kwastomomi.
Kamfanonin sadarwa a Najeriya sun fara rufe layukan wayoyi wadanda ba a sanya musu lambar NIN ba. Ga hanyoyin yadda ake bude layin MTN da aka rufe.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar hallaka mayakan kungiyar ta'addanci ta Boko Haram a jihar Borno. Sojojin sun hallaka 'yan ta'adda takwas.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari