An Karrama Marigayi Sanata, Majalisar Amurka Ta Ƙaƙaba Sabon Takunkumi kan Rasha

An Karrama Marigayi Sanata, Majalisar Amurka Ta Ƙaƙaba Sabon Takunkumi kan Rasha

  • Majalisar Dattawan Amurka ta amince da wani sabon kudirin kakaba takunkumi kan Rasha da kuri’u 86-11, wanda aka sanya wa sunan marigayi Sanata Lindsey Graham
  • Kudirin zai kakaba takunkumi kan manyan jami’an gwamnatin Rasha, ciki har da Vladimir Putin, kamfanonin gwamnati da masu tallafa wa masana’antar tsaro
  • Haka kuma, kudirin zai iya sanya harajin kashi 100% kan manyan kasashe biyar da ke sayen danyen man Rasha, ciki har da China da India.Cikakkiyar fassara

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Washington DC, US - Majalisar Dattawan Amurka ta amince da wani gagarumin kudirin dokar takunkumi kan Rasha, wanda aka sanya wa sunan marigayi Sanata Lindsey Graham.

Graham ya taka muhimmiyar rawa wajen shafe sama da shekara guda ana tattaunawa kan kudirin, kafin daga bisani Sanatoci daga jam’iyyu biyu su amince da shi.

Kara karanta wannan

Kano ta ware N300m na auren gata, an fadi yadda kowace amarya za ta samu

Majalisar Amurka ta tabbatar da sabon takunkumi kan Rasha
Sanatan Amurka, Lindsey graham da Shugaba Donald Trump. Hoto: Donald J Trump, Lindsey graham.
Source: Facebook

Kuri’ar karshe a Majalisar Dattawa ta kasance 86-11. Yanzu kudirin zai bukaci amincewar Majalisar Wakilai, wadda ke hutun aiki har zuwa watan Satumba, cewar The Guardian..

Manufar kudirin kan Rasha

Kudirin zai tilasta sanya takunkumi kan manyan jami’an gwamnatin Rasha, ciki har da Shugaban Rasha Vladimir Putin, da hamshakan ‘yan kasuwar kasar.

Haka kuma, takunkumin zai shafi kamfanonin da gwamnatin Rasha ta mallaka da kuma kamfanonin kasashen waje da ke tallafa wa masana’antar tsaron kasar.

Bugu da kari, kudirin zai iya sanya harajin da ya kai kashi 100% kan manyan kasashe biyar da ke sayen danyen man fetur da iskar gas daga Rasha.

Kasashen da za a sanya wa wannan haraji sun hada da China da India, yayin da Wakilin Kasuwancin Amurka Jamieson Greer zai tantance ainihin adadin harajin.

Sai dai kudirin ya ba da damar keɓe kasashen da ke shigo da kasa da kashi 15% na jimillar iskar gas da Rasha ke fitarwa.

Kara karanta wannan

Yadda gwamnatin marigayi Buhari ta kashe N1.16trn na tallafin man fetur

Hakan zai shafi kasashen da kuma ke kokarin rage amfani da iskar gas daga Rasha cikin wani muhimmin mataki, cewar NBC News.

An amince da kudirin kakaba takunkumi kan Rasha
Marigayi sanatan Amurka da ke goyon bayan kakaba takunkumi kan Rasha kafin rasuwarsa. Hoto
Source: Twitter

Abin da marigayin ya ce kafin rasuwarsa

Kwana guda kafin rasuwarsa, Graham ya sanar da cewa gwamnatin Amurka da manyan Sanatocin da ke mara wa kudirin baya sun cimma matsaya kan dokar.

Ya yi wannan sanarwar ne yayin da yake tsaye a gaban tankokin yaki a titunan Kyiv, babban birnin Ukraine, inda aka shafe dogon lokaci ana tattaunawa.

Bayan rasuwarsa, abokan aikinsa a Majalisar Dattawa sun kara matsa lamba domin amincewa da kudirin, suna bayyana shi a matsayin “abin tunawa mai kyau” da zai bari.

Ya ce:

“Ina da shekaru 32 ina sanin wannan mutumin, kuma zan iya cewa wannan shi ne babbar nasarar Lindsey Graham."

Wicker, wanda shi ne shugaban kwamitin Majalisar Dattawa kan Sojoji, ya bayyana hakan jim kadan bayan rasuwar Graham.

Majalisar Dattawan Amurka ta gudanar da kuri’ar farko kan kudirin ne cikin sa’o’i bayan jana’izar Graham a Washington DC.

Graham: Trump ya gargadi hukumar FBI

Kara karanta wannan

Kano za ta karbi manyan baki, akwai babban taro a kan miyagun kwayoyi

Mun ba ku labarin cewa shugaba Donald Trump na Amurka ya aika sako ga hukumar FBI kan binciken rasuwar Sanata Lindsey Graham.

Trump ya bayyana cewa Graham ya rasu ne sakamakon matsalar lafiya, yana mai cewa mahaifinsa ma ya mutu sakamakon bugun zuciya.

Rahotanni sun nuna Graham ya yi korafin ciwon ƙirji kafin rasuwarsa, yayin da bincike ya nuna tsagewar babban jijiyar jini ce ta yi sanadin mutuwarsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.