'Yan Tijjaniyya daga Kasashen Duniya Sun Turo Sako Ga Tinubu kan Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
- Majalisar Koli ta Tijjaniyya ta duniya ta kai wa Shugaba Bola Tinubu ziyarar ta'aziyya kan rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi a Aso Rock
- Tawagar daga Aljeriya, Najeriya da Senegal ta wakilci sama da mambobi miliyan 400 na darikar a duniya wajen mika sakon ta'aziyya ga Tinubu
- Shugaban Najeriya, Bola Ajmed Tinubu ya yabawa ayyukan addinin Musulunci da darikar Tijjaniyya ke gudanarwa a Afirka da ma duniya baki daya
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Majalisar Koli ta Darikar Tijjaniyya ta duniya ta kai wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ziyara a fadar shugaban kasa da ke babban birnin tarayya Abuja.
Shugabannin darikar Tijjaniyya na duniya sun mika sakon ta'aziyya kan rasuwar marigayi Sheikh Dahiru Bauchi, tsohon jagoran darikar Tijjaniyya a Najeriya ga Shugaba Tinubu.

Source: Twitter
Tawagar Tijjaniyya ta ziyarci Bola Tinubu
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai taimaka wa shugaban kasa na mussmman kan harkokin midiya da sadarwa, Sunday Dare ya wallafa a shafin X yau Juma'a, 7 ga watan Agusta, 2026.
Tawagar ta kunshi wakilai daga kasashe uku, Aljeriya, Najeriya da Senegal, tare da mambobin Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi karkashin jagorancin Khalifa Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Usman Bauchi.
An bayyana cewa tawagar tana wakiltar sama da mambobi miliyan 400 na darikar a duniya.
Khalifan Tijjaniyya ya isar da sakon ta'aziyya
Khalifan Darikar Tijjaniyya daga Aljeriya, Sheikh Ali Bin Arabi, ne ya isar da sakon ta'aziyyar ga Shugaba Tinubu a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja.
Sheikh Ali Bin Arabi ya bayyana irin kyakkyawar alakar da ke tsakanin Najeriya da Aljeriya, yana mai cewa za su ci gaba da yin addu'ar dorewar alakar addini tsakanin kasashen biyu.
Ya kuma yi wa Shugaba Bola Tinubu addu'ar samun zaman lafiya, soyayya, lafiya ta jiki da ta ruhaniya.
Tinubu ya yabawa darikar Tijjaniyya
Da yake mayar da martani, Shugaba Tinubu ya gode wa tawagar bisa ziyarar ta'aziyyar.
Bola Tinubu ya ce:
"Muna matukar kewar mahaifinmu, Sheikh Dahiru Bauchi. Ya kasance uba abin kauna kuma babban jagora."
Shugaban kasar ya kuma yabawa Darikar Tijjaniyya kan ayyukan da take yi wajen yada addinin Musulunci.
"Ina girmama ku saboda abin da kuke yi domin Musulunci a fadin Afirka da ma duniya baki daya. Allah Ya ci gaba da yi muku jagora," in ji shi.

Source: Twitter
Sheikh Dahiru Bauchi ya rasu a 2025
Bayanai sun nuna cewa cewa Sheikh Dahiru Bauchi ya rasu ne a ranar 26 ga Nuwamba, 2025, yana da shekaru 98 a duniya.
Rasuwar babban malamin ta jawo hankalin duniya, inda aka rika turo sakon ta'aziyya daga ciki da wajen Najeriya.
Abin iyalan Dahiru Bauchi suka fadawa Tinubu
A wani labarin, kun ji cewa iyalan fitaccen malamin addinin Musulunci, marigayiSheikh Dahiru Usman Bauchi , sun bayyana mutanen da suka amfani da koyarwarsa.
Iyalan sun bayyana cewa mahaifinsu ya yi jagoranci tare da tarbiyya ga Musulmi sama da miliyan 63 a fadin Najeriya da wasu sassan duniya a tsawon rayuwarsa.
Sun bayyana hakan ne lokacin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kai ziyarar ta’aziyya biyo bayan rasuwar babban malamin addinin.
Asali: Legit.ng

