Manyan Labarai A Yau
Gwamnatin Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) ta tabbatar da mutuwar mutum shida da raunaka wasu sama da 20 a hare-haren da Iran ta kai kasar ta Gabas ta Tsakiya.
Iran ta kai hare-hare kan dakarun sojojin Amurka a kasar Kuwait bayan fara yakin da ya barke a ranar, 28 ga watan Fabrairun 2026. Sojoji sun shiga mawuyacin hali.
Tsohon shugaban kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN), Samson Ayokunle, ya ragargaji manufofin gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu. Ya ce ana talaucewa.
Dakarun ruwa na rundunar IRGC sun kai farmaki kan wasu jiragen ruwa na Isra'ila. Sun bayyana cewa sun kai farmakin ne bayan sun yi biris da gargadin da aka yi musu.
Kasar Spain ta yi Allah wadai da hare-haren Isra'ila da Amurka kan kasar Iran. Yayin da ake ci gaba da yakin, Spain ta janye jakadanta daga kasar Isra'ila.
Rundunar IRGC ta kasar Iran ta ba da sanarwar cewa ta kaddamar da hari mafi zafi kan Isra'ila tun farkon fara yaki. Ta bayyana cewa an kwashe sa'o'i ana kai hari.
Matatar Dangote ta sanar da rangwame a farashin kowace litar fetur, tare da rage litar dizal a Najeriya, wannan ne karo na farko bayan tashin danyen mai a duniya.
Shugaban Majalisar tarayyar Turai, Antonio Costa ya bayyana bisa abubuwan da ke faruwa a kasuwar duniya, Rasha ta fi amfana da yakin Iran, Amurka da Isra'ila.
Kotun daukaka kara ta zartar da hukunci a shari'ar da ake yi da gwamnan jihar Ondo, Lucky Aiyedatiwa, kan bukatar sake neman wa'adi na uku a kan mulki.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari