Manyan Labarai A Yau
Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar LP a zaben 2023, Peter Obi, ya yi tsokack kan babban zaben 2027. Ya gano wanda ya cancanci ya shugabanci Najeriya.
Allah ya yi wa shugaban karamar hukumar Yusufari a jihar Yobe rasuwa. Alhaji Baba Abba Aji, ya rasu ne bayan ya yi fama da jinyar rashin lafiya a kasar waje.
Wani abin fashewa ya tashi a wani asibiti da ke.jihar Kebbi da sanyin safiya. 'Yan sanda sun bazama wajen gudanar da bincike domin gano abin da ya faru.
Wata kungiya mai suna National Grassroots Movement (NGM), ta fito ta yi zargi kan shirin da ta ce ana yi domin tsige shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio.
Rahotanni sun nuna cewa ma'aikatan NTA shida da wasu mutum daya dan jarida sun mutu a hanyar dawowa daga wurin daura aure a titin Gombe zuwa Yola.
Kasar Amurka ta kawo hare-hare ta sama kan 'yan ta'adda a Najeriya. An kai hare-haren ne a Sokoto. Atiku Abubakar na daga cikin manyan da suka yi martani kan harin.
Dan majalisa a kasar Amurka, Riley Moore, ya yi tsokaci kan harin da Donald Trump ya ba da umarnin a kawo Najeriya. Ya ce an yi hakan ne don zaman lafiya.
Wasu 'yan bindiga dauke da makamai sun kai kazamin hari a jihar Kebbi. Ana fargabar mutane da dama sun rasa rayukansu. Wasu da dama sun tsere zuwa daji.
Dakarun sojojin saman Najeriya sun kai hare-hare kan maboyar 'yan ta'adda a jihar Zamfara. Sojojin sun kashe tsageru masu yawa tare da lalata sansanin 'yan bindiga.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari