Manyan Labarai A Yau
Rundunar sojojin Najeriya ta fito ta yi martani kan wasu rahotanni masu cewa dakarunta na shirin yin bore saboda karancin albashi. Ta bayyana yadda lamarin yake.
Rahotanni sun nuna cewa kananan yan kwangila da suka fito zanga zanga a Abuja sun toshe ma'aikatar kudi, sun hana karamar minista, Doris Uzoka-Anite shiga ofis.
Wani jirgin sama na kamfanin Qatar Airways ya yi saukar gaggawa jim kadan bayan tashinsa a filin jirgin kasa da kasa a Legas, babu wanda ya ji rauni.
Kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN), ta yi alhinin rasuwar malamin addinin Musulunci, Imam Abubakar Abdullahi, wanda ya ceci Kiristoci lokacin rikicin Plateau.
Wasu matafiya sun taka bam da ake zargin 'yan ta'adda sun dasa a jihar Zamfara. Lamarin ya jawo an samu jikkatar mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba.
'Yan bindiga dauke da makamai sun kai hari ta'addanci a karamar hukumar Sabon Birni ta jihar Sokoto. Sun kashe mutane tare da raunata bayin Allah.
Tsohon ministan sufuri kuma tsohon gwamnan jihar Rivers, Rotimi Amaechi, ya bayyana cewa 'yan adawa su kuka da kansu kan rashin nasarar da suke yi a zabe.
Gwamnan jihar Edo, Monday Okpebholo, ya dauki matakin kokar daya daga cikin hadimansa. Korar da aka yi masa na da nasaba da zanga-zangar da aka yi a jihar.
Babban jami'in kula da walwala na tafiyar Kwankwasiyya, Saddam Sani Umar, ya bayyana cewa sauya shekar Gwamna Abba Kabir zuwa APC ba za ta jawo asara a Kwankwaso ba.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari