Manyan Labarai A Yau
Hedkwatar rundunar sojojin Iran ta umarci manyan hafsoshi su kara sa ido kan yiwuwar shigar da dakarun makiya cikin kasar bayan barazanar Shugaba Donald Trump.
Tsohon sanata mai wakiltar Kogi ta Yamma a majalisar dattawan Najeriya, Sanata Dino Melaye, ya yi maganganu kan shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu.
Ma'aikatar harkokin wajen Iran ta tabbatar da cewa ta samu sako kan batun tsagaita wuta ta hannun masu shiga tsakani, ta ce za ta yi nazari a kai tukunna.
Sani Buhari, wanda aka fi sani da Sarki Waspapping ya musanta zargin da ake cewa NSA je ya tura aka kama shi kan maganar da ya yi game da yakin Iran da Isra'ila.
Dan majalisar wakilan Amurka, Riley Moore, ya koka kan yawan kashe-kashe a Najeriya. Ya bayyana matakin da Amurka za ta dauka kan lamarin na kashe-kashe.
Hukumomin agajin gaggawa na Isra'ila sunn tabbatar da cewa akalla mutane 14 ne suka samu raunuka sakamakon harin makami mai linzami a kusa da birnin Tel Aviv.
Tsohon dan takarar shugaban kasa a zaben shekarar 2023, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya gana da tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya, Atiku Abubakar.
Jam'iyyar ADC mai adawa a Najeriya ta fito ta nuna yatsa ga gwamnatin APC mai mulki a Najeriya. Ta zarge ta da yunkurin shirya mata bita da kulli.
An gurfanar da mutane hudu da ake zargi da kisan Fatima Abubakar da 'ya'yanta shida a unguwar Dorayi Chiranci a jihar Kano, bangaren gwamnati sun shirya.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari