'Kuri'u 16 Ka Samu': Davido da Bashir Ahmad Sun Kaure da Faɗa, Sun Ƙunyata Juna

'Kuri'u 16 Ka Samu': Davido da Bashir Ahmad Sun Kaure da Faɗa, Sun Ƙunyata Juna

  • Mawaki David Adeleke Davido da Bashir Ahmad sun yi musayar kalamai masu zafi a X bayan cece-kuce ana shirin zaben jihar Osun
  • Mawakin da aka fi sani da Davido ya yi wa Bashir Ahmad gori kan kuri'u 16 da ya samu a zaben fitar da gwani na APC a Kano
  • Davido ya mayar da martani, lamarin da ya jawo muhawara kan siyasa da nishadi yayin da ake tunkarar zaben gwamnan Osun na 2026

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Takaddama ta kaure a dandalin sada zumunta tsakanin fitaccen mawaki, David Adeleke wanda aka fi sani da Davido, da tsohon hadimin shugaban kasa, Bashir Ahmad.

Muhawarar ta fara ne daga batun siyasar zaben gwamnan Osun na 2026, amma daga baya ta koma kan tarihin Davido a gasar Grammy.

Kara karanta wannan

Adeleke ya zargi EFCC da shirin yi wa gwamnatinsa illa gabanin zaɓen Osun

Davido da Bashir Ahmad sun kaure da cacar baki
Tsohon hadimin shugaban kasa, Bashir Ahmad. Hoto: Bashir Ahmad.
Source: Twitter

A wani sako da ya wallafa a X, ya ce an yi ta magana kan yawan kuri'un da ya samu, yanzu kuma a tattauna yawan lambobin yabo na Grammy da Davido ya lashe daga cikin nadin sau biyar da aka yi masa.

Bashir Ahmad ya soki mataki Davido

Lamarin ya fara ne bayan Bashir Ahmad, wanda ya shiga zaben fitar da gwani na jam'iyyar APC domin neman tikitin takarar a Kano, ya mayar da martani ga masu sukar kuri'u 16 da ya samu.

Davido, wanda kawunsa Gwamna Ademola Adeleke ke da muhimmiyar rawa a siyasar Osun kafin zaben 2026, ya mayar da martani cikin sauri. Mawakin ya yi watsi da kwatancen da Bashir ya yi, inda ya rubuta a X cewa:

"Kuri'a 16 fa kadai ka samu a zaben fitar da gwani da aka yi da kai na APC, ka yi mana shiru a nan."

Kara karanta wannan

Kwankwaso ya yi magana da limaman Katolika suka cire tsoro, sun ja da Tinubu

An kaure da fada tsakanin Davido da Bashir Ahmad
Mawaki Davido da Bashir Ahmad. Hoto: Davido, Bashir Ahmad
Source: Facebook

Martanin da Davido ya yi ga Bashir

Musayar kalaman ta jawo martani da dama a shafukan sada zumunta, inda magoya bayan bangarorin biyu suka fara muhawara kan ko ya dace a kwatanta nasarar siyasa da ta fannin waka.

Yayin da Bashir Ahmad ya yi kokarin jawo hankali kan yadda Davido bai taba lashe Grammy ba duk da nadin sau biyar da aka yi masa, Davido ya karkatar da tattaunawar zuwa sakamakon zaben fitar da gwani na APC inda Bashir ya samu kuri'u 16 kacal.

Sabuwar wannan musayar kalamai ta kara zafafa tattaunawar siyasa da ke kewaye da zaben gwamnan Osun na 2026, tare da nuna yadda kafafen sada zumunta ke ci gaba da hade batutuwan siyasa da nishadi a Najeriya.

Sabuwar wannan musayar kalamai ta kara zafafa tattaunawar siyasa da ke kewaye da zaben gwamnan Osun na 2026, tare da nuna yadda kafafen sada zumunta ke ci gaba da hade batutuwan siyasa da nishadi a Najeriya.

Kara karanta wannan

"Ni masoyinsa ne": Davido ya faɗi yadda ya ke musayar sakonni da Ronaldo

Rarara ya caccaki mawaki Davido

Mun ba ku labarin cewa babban mawakin da ke yi wa jam'iyyar APC waka, Dauda Kahutu Rarara ya yi magana game da rashin tsaro da ya addabi tarayyar Najeriya.

Rarara ya magantu ne bayan fitaccen mawakin Najeriya da aka fi sani da Davido ya nuna sunayen daliban Oyo da aka sace a Amurka.

Dauda Kahutu ya nuna rashin jin dadi game da abin da Davido ya yi, yana cewa hakan zubar da mutuncin Najeriya ne a idon duniya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Rahaman Abiola avatar

Rahaman Abiola (Editor-in-Chief) Rahaman Abiola is a Nigerian journalist, editor, and media trainer with a decade of experience stranding diverse roles in both traditional and digital media. As the Editor-in-Chief of LEGIT.ng, he leads content direction with data-driven editorial practice, demonstrating a commitment to modern newsroom management and mentoring team(s) of professionals through audience-centric innovation. His work involves leveraging social media and emerging technologies towards impactful journalism, media innovation, etc. Contact via: rahaman.abiola@corp.legit.ng.