Cikakken Jerin Kasashe 44 da 'Yan Najeriya Za Su iya zuwa ba Tare da Biza ba

Cikakken Jerin Kasashe 44 da 'Yan Najeriya Za Su iya zuwa ba Tare da Biza ba

  • Fasfon Najeriya ya sauka zuwa matsayi na 90 a sabon jadawalin Henley Passport Index, amma har yanzu yana ba da damar shiga kasashe 44
  • Najeriya ta samu maki 44 na shiga kasashe ba tare da neman biza tun kafin tafiya ba, ciki har da kasashen Afirka da yankin Caribbean
  • Masana sun bukaci matafiya su tabbatar da sharuddan shigar kowace kasa, domin wasu na bayar da visa bayan isa ko e-visa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da takwas a aikin jarida.

Abuja - Fasfon Najeriya ya sauka zuwa matsayi na 90 a sabon jadawalin Henley Passport Index na watan Yulin 2026, amma har yanzu masu rike da shi na iya shiga kasashe 44 ba tare da samun biza kafin tafiya ba.

Sabon rahoton da Henley & Partners ta fitar ranar Talata ya nuna cewa fasfon Najeriya ya samu maki 44 na shiga kasashe ba tare da neman biza tun kafin tafiya ba.

Kara karanta wannan

Kasashe 13 na Afrika da Lebanon ke ba biza bayan sun isa kasar

Darajar fasfon Najeriya ta sauka zuwa 90, amma mai rike da shi zai iya zuwa kasashe 44 ba tare da biza ba
Shugaba Bola Ahmed Tinubu (hagu) da fasfon kasar Najeriya na ECOWAS. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Darajar fasfon Najeriya ya sauka

Jadawalin Henley Passport Index na tantance fasfofi 199 bisa yawan kasashen da masu rike da su za su iya shiga ba tare da biza ba, ta amfani da bayanan Hukumar Sufurin Jiragen Sama ta Duniya (IATA).

Najeriya ta kasance a matsayi na 90 a duniya, bayan ta sauko daga matsayi na 89 da ta kasance a rahoton watan Afrilu na shekarar 2026.

Sai dai duk da wannan sauyin matsayi, makinta na shiga kasashe 44 bai canza ba.

Rahoton ya kuma nuna cewa Najeriya ta samu ci gaba idan aka kwatanta da shekarar 2025 da ta kasance a matsayi na 94 da kuma shekarar 2021 lokacin da ta kasance a matsayi na 103.

Kasashen da 'yan Najeriya za su iya shiga

Rahoton ya ce masu fasfon Najeriya na iya shiga wadannan kasashe ba tare da biza kafin tafiya ba, ko kuma su samu biza bayan isa ko e-visa:

Kara karanta wannan

Tinubu ya biya N501bn daga bashin lantarki, ya kaddamar da sabon shirin N729bn

  1. Barbados
  2. Benin
  3. Burkina Faso
  4. Burundi (biza bayan isa)
  5. Cambodia (biza bayan isa)
  6. Cameroon
  7. Cape Verde
  8. Chadi
  9. Comoros (biza bayan isa)
  10. Cook Islands
  11. Côte d’Ivoire
  12. Djibouti
  13. Dominica
  14. Fiji
  15. Ghana
  16. Guinea
  17. Guinea-Bissau
  18. Haiti
  19. Iran (biza bayan isa)
  20. Kenya
  21. Kiribati
  22. Lebanon
  23. Liberia
  24. Madagascar (biza bayan isa)
  25. Maldives (biza bayan isa)
  26. Mali
  27. Mauritius
  28. Micronesia
  29. Montserrat
  30. Mozambique
  31. Nijar
  32. Niue (biza bayan isa)
  33. Palau Islands (biza bayan isa)
  34. Rwanda
  35. Samoa (biza bayan isa)
  36. Senegal
  37. Seychelles
  38. Sierra Leone
  39. St. Kitts and Nevis
  40. Gambia
  41. Timor-Leste (biza bayan isa)
  42. Togo
  43. Tuvalu
  44. Vanuatu
Darajar fasfon Najeriya ta fado zuwa 90 yayin da kaashe 44 suka ba 'yan kasar damar shiga ba tare da biza ba
Fasfon ECOWAS wanda 'yan Najeriya ke amfani da shi a tafiye tafiye zuwa kasashen waje. Hoto: Getty Images
Source: UGC

An gargadi matafiya

Rahoton ya bayyana cewa ba dukkan kasashen ke ba da cikakkiyar shiga ba tare da biza ba, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Wasu kasashen na bayar da biza bayan isa, yayin da wasu ke bukatar matafiya su nemi e-visa kafin tafiya.

Saboda haka, an shawarci 'yan Najeriya da su tabbatar da sabbin sharuddan shige da fice na kasar da suke son ziyarta kafin su shirya tafiya.

Yadda ake sabunta fasfon Najeriya

A wani labari, mun ruwaito cewa, hukumar NIS ta fitar da sabon tsarin sabunta fasfo ga 'yan Najeriya mazauna kasashen waje ta hanyar kai-da-kai ba tare da zuwa ofishin jakadanci ba.

Sabon tsarin ya bai wa masu cancanta damar yin rajistar bayanan tantance su ta manhajar da hukumar ta samar, kuma za su hakan cikin sauki.

Hukumar ta ce wadanda ba su cancanci amfani da tsarin ba ne kawai za su ci gaba da yin rajistar ganawar kai tsaye a ofisoshin jakadancin Najeriya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com