Manyan Labarai A Yau
Netanyahu ya ce shiga yarjejeniyar Abraham Accords da Saudi Arabiya za ta zama babban ci gaba ga zaman lafiya, yayin da Trump ya danganta yarjejeniyar nukiliya.
Yan bindiga sun kashe akalla manoma 23 a Sauna/Ruwan Gora da ke jihar Zamfara, lamarin da ya jefa mazauna yankin cikin firgici tare da ƙara barazanar matsalar abinci
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke wa mutum uku daurin rai da rai bayan sun amsa laifin hannu a garkuwa da dalibai, malamai da kuma alaka da ta'addanci.
Tsohon gwamnan Legas, Babatunde Fashola, ya ce ya fi son ba Tinubu shawara a sirrance maimakon sukar gwamnatinsa a bainar jama’a saboda yana da damar tuntuɓarsa.
Rundunar Sojin Najeriya ta ce wani harin jirgi mara matuƙi a Kila Bariya ya kashe sama da ’yan ISWAP 20 tare da lalata babura sama da 30 da ma’ajiyar abinci.
'Yan takara shida sun fara fafatawa domin maye gurbin António Guterres a Majalisar Dinkin Duniya, yayin da za a fara kada kuri'ar farko a ranar 30 ga Yuli.
Rahotanni sun bayyana cewa akalla mutane 5,700 sun mutu sakamakon mummunar guguwar zafi da ta afku a wata ƙasa ta Turai, a cewar hukumar lafiya ta kasar.
Mataimakin shugaban majalisar wakilan Najeriya, Benjamin Kalu, ya musanta cewa an ware N1bn a kasafin 2026 domin sayo kayan kida ga coci-coci a mazabarsa.
Rikicin Majalisar Dokokin Ondo ya ƙara tsananta yayin da ’yan majalisa 21 suka ba Kakakin Majalisar, Olamide Oladiji, wa’adin yin murabus ko fuskantar tsige shi.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari