Bayan Sharadin Trump, Netanyahu Ya Yi Magana kan Kulla Yarjejeniya da Saudiyya

Bayan Sharadin Trump, Netanyahu Ya Yi Magana kan Kulla Yarjejeniya da Saudiyya

  • Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce shigar Saudiyya cikin yarjejeniyar Abraham zai zama babban ci gaba ga zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya
  • Trump ya ce yarjejeniyar nukiliyar farar hula da Saudiyya ta dogara ne kan shiga yarjejeniyar Abraham da daidaita hulɗa da Isra’ila
  • Riyadh ta ce ba za ta amince da Isra’ila ba har sai an samar da ingantacciyar hanyar kafa ƙasar Falasɗinawa mai cin gashin kanta

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Birnin Tel-Aviv, Israila - Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya yi magana kan yiwuwar daidaita alaka da kasar Saudiyya.

Benjamin Netanyahu ya ce idan Saudiyya ta shiga cikin yarjejeniyar Abraham, hakan zai zama “babban tarihi wajen samun ci gaba ga zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya”.

Netanyahu ya yi magana kan Saudiyya
Benjamin Netanyahu na jawabi a wajen taro Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Netanyahu ya bayyana hakan ne a cikin wata gajeruwar sanarwa da ofishinsa ya fitar ranar Alhamis, 23 ga watan Yulin 2026 a shafin X.

Kara karanta wannan

Trump ya gindaya sharuda ga Saudiyya game da Isra'ila bayan ƙulla yarjejeniya

Me Netanyahu ya ce kan yarjejeniyar?

Netanyahu ya ce haɗin gwiwar sojojin Amurka da Isra’ila wajen kai hari kan gwamnatin Iran da kuma murƙushe ƙungiyoyin ta’addanci da ke da alaƙa da Iran ya samar da damar faɗaɗa da’irar zaman lafiya.

Ya rubuta cewa:

“Kamar yadda Shugaba Trump ya ce, shigar Saudiyya cikin yarjejeniyar Abraham zai zama babban tarihi wajen samun ci gaba ga zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya. Zaman lafiya ta hanyar ƙarfi.”

A farkon yau, Shugaba Donald Trump ya bayyana cewa yarjejeniyar nukiliyar da gwamnatinsa ta rattaba hannu da Saudiyya a wannan makon tana da wani sharadi, wato Saudiyya ta shiga yarjejeniyar Abraham tare da daidaita hulɗarta da Isra’ila.

Ya ce yarjejeniyar nukiliyar farar hula da Ma’aikatar Makamashi ta Amurka ke kulla wa da Saudiyya, wadda za ta kasance ne domin amfanin farar hula ba na soja ba, za a amince da ita ne kawai idan Saudiyya ta shiga cikin yarjejeniyar Abraham.

Kara karanta wannan

Shirin Amurka na samar wa Saudi nukiliya ya firgita 'yan Isra'ila

Trump ya ƙara da cewa Amurka ba ta adawa da cibiyoyin nukiliya na farar hula da ba sa amfani da makamashin nukiliya da aka inganta.

Amurka za ta taimakawa Saudiyya

A daren jiya, Amurka ta sanar a hukumance cewa ta rattaba hannu kan yarjejeniyar haɗin gwiwa da Saudiyya, wadda za ta bai wa Riyadh cikakken taimako wajen haɓaka shirin nukiliya domin amfanin farar hula.

Rahotanni sun ce yarjejeniyar za ta ci gaba da aiki na tsawon shekaru 30, kuma za ta bai wa kamfanonin Amurka damar ba da rance da kuma gina tashoshin samar lantarki na nukiliya a Saudiyya.

A ƙarƙashin yarjejeniyar, an kuma tsara wata hanya ta sanya ido wadda za ta yi aiki kai tsaye da gwamnatin Amurka, ba tare da aiki tare da Hukumar Kula da Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA) ba.

Netanyahu ya yi maganar Saudiyya
Shugaban kasar Israila, Benjamin Netanyahu Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Riyadh ba ta tanka ba

Har zuwa yanzu, mahukunta a Riyadh ba su mayar da martani a bainar jama’a kan kalaman Trump ba.

Sai dai Saudiyya ta sha nanata cewa ba za ta amince da Isra’ila ba har sai an samar da ingantacciyar hanyar kafa ƙasar Falasɗinawa mai cin gashin kanta.

Kara karanta wannan

'Mun rike wuta': Ministan Amurka ya yi Ikirarin Iran na rokon a yi sulhu

Trump bai bayyana cewa yarjejeniyar ta dogara ne kan Saudiyya ta shiga yarjejeniyar Abraham ba lokacin da aka sanar da ita a ranar Laraba.

A halin yanzu, Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), Bahrain, Sudan, Morocco da Kazakhstan ne ke cikin ƙasashen da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar Abraham.

Batun cafke Netanyahu a Amurka

A wani labarin kuma, kun ji cewa shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana cewa ba za a kama Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu ba idan ya kai ziyara ƙasar Amurka.

Shugaba Donald Trump ya bayyana ya jaddada cewa babu wani yanayi da zai sa a cafke Netanyahu yayin da yake a kasar Amurka.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng