Manyan Labarai A Yau
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya yi alhini kan asarar rayuka da dukiyoyi da aka samu sakamakon ambaliyar ruwan da ta auku a johohi masu yawa na kasar nan.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar hallaka wasu 'yan bindiga a jihar Kaduna. Sojojin sun kuma cafke wani daga cikin mai ba 'yan bindigan bayanai.
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya yiwa jigon PDP Bode George martani kan shawarar da ya ba shi ta ya hakura da yin takara a 2027.
Hukumar da ke kula da ƴan Najeriya mazauna kasahen waje ta gano bayanan matar da aka ji a bidiyo tana barazanar ƙarar da yarbawa mazauna ƙasar Kanada.
An gudanar da jana'izar da sojan ruwan Najeriya, Laftanal Kwamanda Gideon Yashim Gwaza, wanda ya rasu yayin ceto wasu mutane da jirginsu ya kusa nutsewa.
Gwamnatin Najeriya ta sake turawa yan kasar Poland da jami'an tsaro suka kama bisa zargin daga tutar Rasha a lokacin zanga zangar adawa da tsadar rayuwa a Arewa.
Gwamnan jihar Kogi, Ahmed Usman Ododo, ya yi nade nade a gwamnatinsa. Gwamnan na jam'iyyar APC ya nada sababbin manyan sakatarori guda 12 a jihar.
Gwamnatin tarayya ta shiga zama da wakilan kungiyar malaman jami'o'i ta kasa (ASUU) kan shirin da suke yi na tsunduma cikin yajin aiki a fadin kasar nan.
Hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) reshen jihar Ondo , ta tabbatar da aukuwar wani mummunan hatsarin mota wanda ya salwantar da rayukan mutum16.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari