Manyan Labarai A Yau
Tsohon dogarin marigayi Janar Sani Abacha, Manjo Hamza Al-Mustapha (mai ritaya), ya karyata labarin da ake yadawa kan abin da ya kashe tsohon shugaban kasar.
Farfesa Ango Abdullahi da Prof. Usman Bugaje sun ce Arewa ta rasa ƙimominta da shugabanci nagari, suna kira a koma tafarkin Janar Hassan Katsina.
Gwamnan Nasarawa Abdullahi Sule ya sauke masu ba shi shawara na musamman takwas, tare da naɗa wasu tara sabbi, kwana biyu bayan sauke kwamishinoni shida.
Ɗan Majalisar Wakilai Chinedu Obika ya ce wani ɗan majalisa ya kasa samun ₦700,000 na kuɗin makarantar ’yarsa, har sai da ya taimaka masa ya biya.
An gurfanar da ’yar takarar gwamnan Ekiti ta APC, Abimbola Olawumi, kan zargin wallafa saƙonnin barazana a kafafen sada zumunta, yayin da ta musanta zarge-zargen.
Kotun bincike a Landan ta bayyana cewa Yarima Abdullah bin Fahad na Saudiyya ya mutu ne sakamakon haɗa barasa, GHB da magungunan rage damuwa a wani otel.
Olusegun Obasanjo ya zargi tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar da bai wa marigayi Ghali Na’Abba N5m domin fara shirin tsige shi daga mulki.
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya sanar da shirin kafa kamfanin jirgin sama na kasuwanci mallakar jihar domin samar da ayyukan yi ga ’yan asalin Kano.
Ɗan takarar gwamnan Kaduna da ya sha kaye a ADC, Muhammad Bello Mainan Zazzau, ya yi murabus daga jam’iyyar kwanaki bayan sasanta rikicin shugabancinta.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari