Mutuwa Ta Ratsa APC, Mataimakiyar Shugabar Matan Jam'iyyar a Yobe Ta Rasu

Mutuwa Ta Ratsa APC, Mataimakiyar Shugabar Matan Jam'iyyar a Yobe Ta Rasu

  • Mataimakiyar shugabar mata ta jam’iyyar APC a jihar Yobe, Hajiya Fatima Umar Mairiga, ta rasu bayan gajeriyar rashin lafiya
  • An shirya gudanar da sallar jana’izarta a Damaturu, babban birnin jihar, bisa tsarin addinin Musulunci
  • Marigayiyar ta taka muhimmiyar rawa wajen hada kan mata da karfafa goyon bayan jam’iyyar APC a matakin tushe a fadin jihar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Yobe - Mataimakiyar shugabar mata ta jam’iyyar APC a jihar Yobe, Hajiya Fatima Umar Mairiga, ta rasu bayan gajeriyar rashin lafiya.

Fatima Mairiga ta rasu ne a ranar Asabar, 25 ga watan Yulin 2026 a Kano, inda rahotanni suka ce tana karbar magani.

Fatima Mairiga ta bar duniya
Marigayiya Fatima Gwamnati Mairiga Hoto: Gwamnaty Mairiga
Source: Facebook

Sakataren Yada Labarai na Mataimakin Gwamnan Jihar Yobe, Hussaini Suleh, ne ya sanar da rasuwar a cikin wata sanarwa, inda ya bayyana lamarin a matsayin babban rashi ga APC a jihar,.rahoton The Punch ya nuna hakan.

Kara karanta wannan

ADC ta gamu da koma baya, na kusa da El Rufai ya fice daga jam'iyyar a Kaduna

APC ta yi rashin Fatima Mairiga

Sanarwar ta ce mataimakiyar shugabar matan ta APC ta rasu ne bayan gajeriyar rashin lafiya.

“Allah Ya yi wa Hajiya Fatima Mairiga, mataimakiyar shugabar mata ta APC a Jihar Yobe, rasuwa a yau a Kano bayan gajeriyar rashin lafiya,” in ji sanarwar.

Ba a bayyana irin rashin lafiyar da ta yi ba, amma rasuwarta ta jefa ‘yan uwa, abokan siyasa da magoya bayanta cikin jimami.

An sanar da lokacin jana’iza

Sanarwar ta ce za a gudanar da sallar jana’izar marigayiyar a Damaturu, babban birnin Jihar Yobe, bisa tsarin addinin Musulunci.

“Za a gudanar da sallar jana’izar ne ranar Lahadi da karfe 4:00 na yamma a Masallacin Yobe da Cibiyar Musulunci da ke Damaturu, Jihar Yobe,” in ji sanarwar.

Ana sa ran za a binne ta nan take bayan sallar jana’izar, kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

‘Yan uwa, abokan siyasa, mambobin jam’iyya, jami’an gwamnati da masu fatan alheri ne ake sa ran za su halarci jana’izar domin yi wa marigayiyar bankwana na karshe.

Kara karanta wannan

Mace ta samu shiga tikitin takarar shugaban kasar Najeriya a zaben 2027

Da yake addu’ar Allah Ya gafarta mata, kakakin Mataimakin Gwamnan ya ce: “Allah Ya gafarta mata kurakuranta, Ya kuma shigar da ita Aljannatul Firdausi.”

Ta taka rawa a APC

Mairiga ta kasance Mataimakiyar Shugabar Mata ta APC a Jihar Yobe, inda ta taka muhimmiyar rawa wajen hada kan mata da karfafa goyon bayan jam’iyyar a matakin tushe a fadin jihar.

A wani sakon ta’aziyya, shugaban hukumar YEMA, Mohammed Goje, ya bayyana marigayiyar a matsayin shugabar siyasa mai aminci da amana, wadda rayuwarta ta kasance cike da tausayi, jin kai da biyayya.

Fatima Mairiga ta rasu
Fatima Mairiga a wajen taron jam'iyyar APC Hoto: Gwamnaty Mairiga
Source: Facebook
“Cikin tsananin bakin ciki da takaici mai girma na samu labarin rasuwar Hajiya Fatima Umar Mairiga, Mataimakiyar Shugabar Mata ta APC a jihar Yobe."
“Hajiya Fatima ta kasance fiye da shugabar siyasa; amintacciya ce kuma mai aminci wadda rayuwarta ta kasance cike da kyautatawa, tausayi da biyayya."
“Za a tuna da ita saboda karamcinta, gajiyar da ba ta sani ba wajen tallafa wa marayu da marasa galihu, da kuma yadda take kasancewa kafada da kafada da kawayenta da duk wata kyakkyawar manufa da ta yi imani da ita."

Kara karanta wannan

Sokoto: Dan majalisar tarayya ya zama dan takarar mataimakin gwamna a ADC

- Mohammed Goje

Yadda yariman Saudiyya ya rasu

A wani labarin kuma, kun ji cewa Kotun bincike da ke birnin Landan ta bayyana yadda wani dan gidan sarautar Saudiyya, Yarima Abdullah bin Fahad bin Abdullah bin Abdulaziz bin Jalawi Al Saud, ya rasu.

Binciken kotun ya gano cewa marigayin ya mutu ne sakamakon bugun zuciya bayan haɗa barasa da kwayar GHB tare da wasu magungunan rage damuwa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng