Gwamna Ya Maka EFCC a Kotu bayan Rufe Asusun Gwamnatinsa ana Shirin Zaɓe

Gwamna Ya Maka EFCC a Kotu bayan Rufe Asusun Gwamnatinsa ana Shirin Zaɓe

  • Gwamna Ademola Adeleke na jihar Osun ya shigar da ƙara kan hukumar yaki da cin hanci a Najeriya ta EFCC
  • Gwamnatin Osun ta ce EFCC ba ta da ikon daskarar da asusun gwamnati ba tare da umarnin kotu ba, tana mai zargin karya kundin tsarin mulki da dokokin ƙasa
  • Yayin da EFCC ta ce tana binciken zargin karkatar da Naira biliyan 11, Shugaba Bola Tinubu ya umarci hukumar ta garzaya kotu domin a cire takunkumin asusun

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Ibadan, Osun - Gwamnan Osun, Sanata Ademola Adeleke, ya shigar da ƙara a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja kan Hukumar EFCC.

Hakan ya biyo bayan hukumar yaki da cin hanci ta rufe da asusun rabon kuɗaɗen gwamnatin jihar.

Gwamna ya maka EFCC a kotu
Gwamna Ademola Adeleke na jihar Osun. Hoto: Governor Ademola Adeleke.
Source: Instagram

A cikin ƙarar, Adeleke tare da Babban Lauyan Jihar da Akanta Janar sun nemi kotu ta ayyana matakin a matsayin wanda ya saɓa wa doka da kundin tsarin mulki, cewar Channels TV.

Kara karanta wannan

"Na ji kunya": Tinubu ya ba EFCC umarnin bude asusun gwamnatin Osun da aka rufe

An sanya EFCC, shugaban hukumar da First Bank Nigeria Limited a matsayin waɗanda ake ƙara. Masu ƙarar sun ce EFCC ba ta da ikon sanya takunkumi ko umarnin post no debit kan asusun gwamnatin jihar ba tare da samun ingantaccen umarnin kotu ba, kamar yadda kundin tsarin mulki da dokokin EFCC da dokar hana safarar kuɗi suka tanada.

Sun kuma roƙi kotu ta tantance ko umarnin da EFCC ta aika wa bankin a ranar 5 ga Agustan 2026 na daskarar da asusun gwamnatin Osun ya kasance bisa doka.

A cewarsu, matakin ya zama amfani da iko ba bisa ka'ida ba, tare da tauye ikon gwamnatin jihar da hana jama'a cin moriyar dimokuraɗiyya.

Masu ƙarar sun ce First Bank ma bai kamata ya aiwatar da umarnin EFCC ba tare da sahihin umarnin kotu ba.

Sun bayyana cewa matakin ya hana gwamnatin jihar gudanar da ayyukanta na kundin tsarin mulki, wanda zai iya shafar biyan ma'aikata da aiwatar da ayyukan gwamnati.

Saboda haka, sun roƙi kotu ta ayyana daskarar da asusun a matsayin haramtacciya kuma marar inganci.

Sun kuma nemi a soke duk wani takunkumi da aka sanya kan asusun tare da umartar bankin ya ba gwamnatin Osun damar ci gaba da amfani da asusun ba tare da wani cikas ba.

Kara karanta wannan

Dalilan EFCC na garkame asusun gwamnatin Osun kafin zabe

Baya ga haka, sun nemi kotu ta hana EFCC da jami'anta sake daskarar da kowane asusun gwamnatin Osun ba tare da bin tanadin doka ba.

Haka kuma sun buƙaci a hana First Bank bin duk wata wasiƙa ko umarni daga EFCC da ba ta samu amincewar kotu ba.

Gwamnatin Osun ta kuma nemi kotu ta ba ta diyyar Naira biliyan biyu a matsayin tara da diyya saboda abin da ta kira tsoma baki ba bisa ƙa'ida ba cikin kuɗaɗen jama'a.

Ta kuma nemi a umarci waɗanda ake ƙara su biya kuɗin shari'ar.

Har yanzu kotu ba ta sanya ranar sauraron ƙarar ba, an shigar da ita ne jim kaɗan bayan Shugaba Bola Tinubu ya umarci EFCC da ta garzaya kotu domin a cire takunkumin da aka sanya wa asusun rabon kuɗaɗen gwamnatin Osun.

A ranar Laraba, EFCC ta tabbatar da cewa ita ce ta daskarar da asusun, tana mai cewa matakin yana da alaƙa da binciken zargin karkatar da kuɗaɗen Ecology Funds, Intervention Funds da kuɗaɗen FAAC da ya kai Naira biliyan 11.

Kara karanta wannan

Sarkin Musulmi ya nuna ɓacin ransa kan cin zarafin Musulmai yan ƙabilar Igbo

Hukumar ta jaddada cewa matakin ba shi da alaƙa da zaɓen Osun mai zuwa.

Sai dai Gwamna Adeleke ya bayyana matakin a matsayin wanda ya saɓa wa kundin tsarin mulki.

A nasa ɓangaren, Shugaba Tinubu ya ce abin da ya ba shi kunya ba binciken EFCC ba ne, sai dai lokacin da aka ɗauki matakin, duk da cewa ya ce hukumar ta yi ikirarin samun umarnin kotu.

Meta description:

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.