Labaran Duniya
Zanga zanga mai zafi ta barke a Tel Aviv yayin da yakin Isra'ila da Iran ya shiga mako na 3. Ana ci gaba da kai wa juna hari a rumbunan ajiyar mai da muhimman wurare
Ministan harkokin waje na Iran,Abbas Araghchi ya tabbatar da cewa babu wata matsala a tattare da jagoran addinin kasar, Mojtaba Khamenei bayan ya ji raunuka.
Isra'ila ta kashe Janar Abdullah Jalali Nasab a Tehran. Wannan hari na cikin kamfen din ruguza leken asirin Iran yayin farmakin Operation Roaring Lion.
Jakadan Iran a Rasha, Kazem Jalali, yi yi magana da kakkausa murya kan Amurka. Kazem Jalali ya gargadi Amurka kan ka da ta kashe Mojtaba Khamenei.
Shugaban rundunar sojojin kasar Iran ya sha alwashi kan nutsar da jirgin ruwan Iran da Amurka ta yi a cikin teku. Ya bayyana cewa dole ne za su dauki fansar hakan.
Kungiyar Hezbollah da ke ayyukanta a kasar Lebanon ta kai hare-hare kan Isra'ila. Hezbollah ta kai hare-hare a wurare da dama da suka hada da Arewacon Isra'ila.
Gwamnatin Iran ta jaddada cewa dakarun sojojin juyin juya hali sun shirya tunkarar kowane kalubale a yakin da ake ta musayar wuta da Amurka da Isra'ila.
Amurka ta shirya tura bataliyar sojojin ruwa 2,200 zuwa Gabas ta Tsakiya a cikin jirgin USS Tripoli. Manufar ita ce kare mashigar ruwan Hormuz daga hare-haren Iran.
Daga fara yaki zuwa yanzu, kasashen Amurka da Isra'ila sun hallaka Iraniyawa 1,444 tare da jikkata wasu sama da 18,000, sun kuma lalata gine-gine da cibiyoyi.
Labaran Duniya
Samu kari