Tinubu Ya Tsallake Kansa, Buhari da Yar'adua, Ya Fadi Shugaban da Ya Fi Amfanar Najeriya
- Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon shugaban mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida (mai ritaya), murnar cika shekaru 85
- Tinubu ya ce Babangida ya yi wa Najeriya ayyuka masu matukar tasiri ta hanyoyin da babu wani shugaba da ya taɓa yin hakan
- Shugaban ya bayyana tsohon shugaban sojan a matsayin fitaccen jagora wanda ya bayar da gagarumar gudunmawa ga ci gaban ƙasa
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya taya dattijon ƙasa kuma tsohon shugaban kasa na mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida (mai ritaya), murnar cika shekaru 85 da haihuwa.
Shugaba Tinubu ya bayyana tsohon shugaban a matsayin wanda ya yi wa Najeriya ayyuka masu tasiri ta hanyoyin da babu wani shugaban kasa da ya taɓa yi.

Source: Twitter
Shugaban ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da Bayo Onanuga, mai ba shi shawara na musamman kan yaɗa labarai da dabaru, ya fitar, kamar yadda Daily Trust ta rahoto .
Sakon da Tinubu ya aika wa IBB
Tinubu ya kuma bayyana Janar Babangida a matsayin fitaccen shugaba wanda ƙwarewarsa a aikin soja ta kai ga zama shugaban ƙasar bayan juyin mulkin da aka yi a shekarar 1985.
Shugaban ya ce:
“Ko kuna son sa ko ba ku son sa, tsohon Shugaba Babangida ya yi wa Najeriya tasiri ta hanyoyin da babu wani shugaba da ya taɓa yi. Mulkinsa na tsawon shekaru takwas ya bar abubuwa masu dorewa a fannonin siyasa, tattalin arziki da kuma tsarin ƙasa.
“Ya bunƙasa tattalin arzikin ƙasar, ya samar da ababen more rayuwa masu ɗorewa, sannan ya kafa hukumomi da cibiyoyi da dama waɗanda har yanzu suke ci gaba da yi wa muradun ƙasa hidima.
"Ba don hangen nesansa, hikimarsa da kuma fahimtarsa kan daidaito da adalci ba, da akwai yiwuwar wasu jihohin tarayya da dama ba su wanzu a yau.”
Tinubu ya jinjina wa Babangida
Tinubu ya ce sunan Janar Babangida da gudunmawarsa za su ci gaba da kasancewa a tarihi saboda irin gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban Najeriya.
Shugaban ya ce ko bayan ritayarsa, yayin da yake rayuwa cikin kwanciyar hankali a gidansa da ke Minna Hilltop a Jihar Neja, Janar Babangida na ci gaba da bai wa ƙasa shawarwari masu amfani da jagoranci.
“Shawarwarinsa da hikimarsa na ci gaba da zama abin ƙarfafa wa matasa gwiwa,” in ji Bola Tinubu.

Source: Twitter
A rahoton Vanguard, Tinubu ya ƙara da cewa:
“Ina yi maka fatan samun ci gaba da falala, ƙoshin lafiya da sabon ƙarfi. Allah Maɗaukakin Sarki ya bar ka tare da mu na tsawon shekaru masu yawa masu zuwa.”
Tinubu ya taya Gwamna Adeleke murna
A wani labarin, kun ji cewa shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya taya Gwamna Ademola Adeleke murnar samun nasara a zaben gwamnan jihar Osun na 2026.
Tinubu ya ce sake zaɓar Adeleke wata alama ce da ke nuna cewa dimokuraɗiyya za ta ci gaba da bunƙasa a Najeriya ƙarƙashin mulkin jam’iyyar APC.
Asali: Legit.ng

