Tirkashi: Trump Ya Yi Magana kan Yiwuwar Farmakar Iran da Makamin Nukiliya
- Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya amsa tambayoyin manema labarai a fadar White House a ranar Alhamis, 23 ga watan Afirilun 2026
- An jefo tambayar yiwuwar Amurka ta yi amfani da makamin nukiliya ga Trump, inda ya ba da amsa a take a wajen taron
- Shugaban na Amurka ya bayyana cewa sun ruguza Iran ta hanyar amfani da makamai na yau da kullum ba tare da makamin nukiliya ba
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Birnin Washington, Amurka - Shugaban kasar Amurka, Donald Trump, ya yi magana kan batun yiwuwar kai hari kan Iran da makamin nukiliya.
Shugaba Trump ya yi watsi da batun kai wa Iran hari da makamin nukiliya bayan barazanar da ya yi a baya na ruguza dukkan al'ummar Iran baki ɗaya.

Source: Getty Images
Tashar Fox News ta kawo rahoton cewa Trump ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai a fadar White House a ranar Alhamis, 23 ga watan Afirilun 2026.
Shin Trump zai yi amfani da makamin nukiliya?
Shugaban na Amurka ya bayyana cewa ba ya bukatar amfani da makamin nukiliya domin farmakar Iran.
“A’a, ba zan yi hakan ba. Ba mu buƙatarsa. Me zan yi da shi? Me ya sa za a yi irin wannan sakaryar tambayar?”
“Me ya sa zan yi amfani da makamin nukiliya bayan mun nakasa su ta hanyar amfani da makaman yau da kullum ba tare da shi ba?”
“Makamin nukiliya ba abu ba ne da za a taɓa barin kowa ya yi amfani da shi ba."
- Donald Trump
Amurka ta sha yin gargadi kan Iran
Mataimakin shugaban kasa, JD Vance, a lokacin rikicin, ya yi gargaɗin cewa Amurka a shirye take ta ƙara tsananin barna a kan Iran da makaman da ba a yi amfani da su ba a baya, amma fadar White House ta musanta cewa yana barazanar kai hare-haren nukiliya ne.
Vance, a tattaunawar da aka gaza cimma matsaya, ya matsa wa Iran lamba domin ta ba da ƙarin rangwame kan ayyukanta na nukiliya da ake taƙaddama a kai, jaridar Vanguard ta kawo rahoton.
Trump ya shaida wa manema labarai cewa yana son ganin Iran “ba tare da makamin nukiliya wanda zai yi ƙoƙarin tarwatsa ɗaya daga cikin biranenmu ko kuma tarwatsa yankin Gabas ta Tsakiya baki ɗaya ba.”

Source: Facebook
Iran ta musanta neman kera makamin nukiliya
Iran ta musanta neman makamin nukiliya, kuma hukumar sa ido kan makaman nukiliya ta majalisar dinkin duniya ta ce kera bam ɗin nukiliya ba wani abu ne da ke shirin faruwa ba kafin yaƙin.
Amurka ce kaɗai ƙasar da ta taɓa yin amfani da makaman nukiliya a yaƙi, inda ta ruguza biranen Hiroshima da Nagasaki na Japan a ƙarshen yaƙin duniya na biyu, wanda ya kashe mutane kusan 214,000.
Trump ya yi magana kan mashigar Hormuz
A wani labarin kuma, kun ji cewa shugaban kasar Amurka ya dauko batun kwace ikon mashigar Hormuz daga hannun Iran.
Shugaba Trump ya ce Amurka tana da cikakken iko a kan mashigar ruwa ta Hormuz, wadda take matsayin muhimmiyar hanyar jigilar ɗanyen mai a teku.
Trump ya nuna cewa cikakken iko kan mashigar ruwan ya dawo hannun dakarun sojojin ruwan Amurka da aka jibge a yankin.
Asali: Legit.ng

