Labaran garkuwa da mutane
A halin yanzun tsaro na nema ya gagari babban birnin tarayya Abuja, duk cewa masu kai hari ba su shiga cikin birnin ba, amma ana sace mutane a ƙauyukan Abuja.
Wasu yan bindig dun kai sabon hari kauyuka biyu dake cikin jihar Benuwai, sun kashe mutum11 tareda jikkata wasu da dama. Yan sanda sunce basu samu rahoto ba.
Ɗan majalisar wakilan tarayya daga jihar Kebbi, Kabir Ibrahim Tukura, ya bayyana cewa an kashe aƙalla mutum 500, tare da sace wasu mutum 201 a mazaɓar sa kawai.
Kwamishinan tsaro na jihar Kaduna, Samuel Aruwan, yace bai samu bayani daga hukumomin tsaro ba dangane da kama yan bindigan da suka sace ɗaliban Greenfield.
Yan bindiga Sun kai wasu jerin hare-hare guda biyu a jihohin Zamfara da Kaduna, inda suka hallaka mutum 30 a Zamfara, sannan Suka kashe mutum uku a Kaduna.
Fitaccen malamin addinin Islama, Sheikh Gumi ya bayyana halin da 'yan bindiga ke ciki, in da ya ce tuni sun gaji kuma suna neman zaman lafiya a halin da ake.
Wasu yan bindiga da ake zargin yan Fulani makiyaya ne, sun kai hari wani ƙauye dake yankin ƙaramar hukumar Agatu jihar Benuwai, sun samu nasarar kashe mutum 27.
Wasu yan bindiga sun hallaka mutane aƙalla 26 a wani mummunan hari da suka kai ƙauyukan jihar Zamafa, an fafata tsakanin su da jami'an yan sanda dake yankin.
Wasu yan bindiga sun kutsa kai har cikin gidan Hakimin Zungeru, Alhaji Mustapha Madaki, inda suka yi awon gaba da shi, tare da matan sa biyu, a jihar Neja.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari