Wani Bam da Aka Dasa a cikin Mota Ya Tashi a Wurin Hada Hadar Kasuwanci a Jihar Legas
- Kwamishinan ‘yan sandan Legas ya tabbatar da cewa kasuwar kayayyakin takalma da ke Mushin na cikin aminci bayan fashewar wani bam
- Rahotin binciken farko ya nuna cewa an dasa bam ɗin ƙarƙashin wata mota a kusa da kasuwa, kuma ya fashe ne lokacin da aka kunna ta
- Bayanai sun nuna cewa mutum guda ya samu rauni, yayin da jami’an tsaro suka ce ba a gano wani ƙarin bam a yankin
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Lagos, Nigeria - Kwamishinan ‘Yan Sandan Legas, Fatai Tijani, ya tabbatar da fashewar bam a wani yankin da ake harkokin kasuwanci a jihar, amma jami'an tsaro sun shawo kan lamarin a yanzu.
Tijani ya bayyana hakan ne ranar Litinin yayin da yake zantawa da manema labarai a wurin da lamarin ya faru a Kasuwar Kayayyakin Takalma da ke Mushin, bayan jami’an tsaro sun gudanar da cikakken bincike.

Source: Original
A cewarsa, ‘yan sanda sun samu rahoton fashewar ne kuma nan take suka tura jami’an kwance bama-bamai (EOD) domin killace yankin da kuma tabbatar da tsaro, in ji Daily Trust.
Ya ce:
“Mun tura jami’an EOD bayan mun samu rahoton fashewar. An killace yankin kuma an gudanar da cikakken bincike.”
Yadda aka dasa bam a jihar Legas
Kwamishinan ya bayyana cewa binciken farko ya nuna cewa bam ɗin an dasa shi ne a ƙarƙashin wata mota.
Ya ce an ajiye bam ɗin ne a gefen fasinja na motar, kuma ya fashe ne lokacin da aka kunna injin motar.
"An dasa bam ɗin a ƙarƙashin motar, a gefen fasinja kuma ya fashe ne lokacin da aka kunnata,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa mutum guda ne ya samu rauni a lamarin, kuma an kai shi asibiti inda yake karɓar magani cikin kwanciyar hankali.
Yan sanda sun fara binciken kwakwaf

Kara karanta wannan
Abin tausayi: Ɗan kasuwa ya mutu a wani yanayi a ɗakin fitacciyar 'yar TikTok a jihar Kano
Tijani ya ce bayan cikakken binciken da jami’an kwance bama-bamai suka gudanar, ba a gano wani ƙarin bam a yankin ba.
Ya bayyana cewa an tattara ragowar bam ɗin domin gudanar da binciken kwakwaf yayin da bincike ke ci gaba, kamar yadda jaridar Vanguard ta kawo.

Source: Twitter
Kwamishinan ya buƙaci mazauna jihar su kwantar da hankalinsu tare da yin watsi da jita-jitar da ke yaɗuwa cewa tsaro ya tabarbare a Legas.
Ya kuma sake jaddada aniyar rundunar ‘yan sanda ta kare rayuka da dukiyoyin jama’a a faɗin jihar, yana gargadin masu aikata laifuffuka da su guji Legas.
Bam ya halaka yan sanda a Zamfara
A wani rahoton, kun ji cewa jami’an rundunar ’yan sanda uku sun rasa rayukansu yayin da motarsu ta taka bam kuma ya tashi da su a jihar Zamfara.
Mai taimaka wa gwamnan jihar Zamfara kan harkokin yada labarai, Mugira Yusuf, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar.
Lamarin ya faru ne lokacin da suka fito sintiri a titin Anka zuwa Bagega kuma jami’an da suka mutu kwararru ne a fannin lalata bama-bamai
Asali: Legit.ng
