Katsina
‘Yan bindiga sun sace dalibai 2 a jami’ar FUDMA, da ke jihar Katsina yayin da aka ceto wani wanda aka yi garkuwa da shi a Adamawa, an kuma kama malami a Jigawa.
‘Yan sanda sun kama masu safarar makamai, miyagun kwayoyi da jabun kuɗi a samame daban-daban, inda suka cafke masu hannu a laifuka tare da kayayyakin haram.
Bayan shafe fiye da wata daya a hannun yan bindiga, ana na ci gaba da riƙe Janar Maharazu Tsiga a da aka yi garkuwa da shi tun a farkon watan Fabrairun 2025.
Jami’an tsaro sun dakile wani harin ‘yan bindiga a jihar Katsina, inda suka kashe dan ta'adda daya, sannan suka kwato makamai, babura da sauran kayan aikin miyagun.
Gwamnatin jihar Katsina ta bayyana kudaden fansan da 'yan bindiga suka nema kan matashin mahaddacin Al-Kur'anin da suka sace a kwanakin baya a jihar.
'Yan fashi da makami sun kai hari makarantar sakandare ta Yashe a karamar hukumar Kusada a jihar Katsina. Sun kashe mai gadi a lokacin da ake suhur.
Dakarun sojojin saman Najeriya sun samu nasarar yin luguden wuta kan maboyar 'yan bindiga a jihar Katsina. Sojojin sun hallaka miyaginmasu yawa a farmakin.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun sace wani matashi mahaddacin Al-Kur'ani a jihar Katsina. 'Yan bindigan sun sace shi ne tare da mahaifinsa da 'yan uwansa.
'Yan bindiga sun kafa sansani a Bakori, inda suke kai hare-hare. An rahoto cewa suna kokarin mamaye Tafoki, Faskari, Funtua da Danja, inda jama'a ke tserewa.
Katsina
Samu kari