Katsina: Fusatattun Matasa Sun Cinnawa Fadar Basarake Wuta, An Yi Asara

Katsina: Fusatattun Matasa Sun Cinnawa Fadar Basarake Wuta, An Yi Asara

  • Matasa a garin Tsiga a jihar Katsina sun kone fadar dagacin garin bayan wani barawo ya nemi mafaka a can bayan ya daba wa mai babur wuka
  • Jama’a sun bukaci a mika musu barawon amma aka hana, lamarin da ya tayar da hankali har ya kai ga kona fadar sarautar da ke Tsiga
  • Wanda aka daba wa wuka yanzu yana cikin mawuyacin hali, yayin da lamarin ke kara tayar da kura a yankin karamar hukumar Bakori a Katsina

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Bakori, Katsina - An shiga tashin hankali a garin Tsiga da ke karamar hukumar Bakori a jihar Katsina da ke Arewacin Najeriya.

An ce wasu fusatattun matasa sun cinna wuta a fadar dagacin Tsiga da ke karamar hukumar bayan biyo wani barawo.

Matasa sun kona fadar dagaci a Katsina
Fusatattun matasa sun komawa Katsina. Hoto: Legit.
Asali: Original

Katsina: Dalilin cinna wuta a fadar basarake

Shafin Bakatsine da ke kawo rahoto kan tsaro shi ya tabbatar da haka a dandalin X a jiya Talata 13 ga watan Mayun 2025.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Majiyar ta ce matasan sun cinna wa fadar dagacin Tsiga wuta, bayan wani barawo da ya daba wa mai babur wuka ya tsere ya buya a can.

Jama’an gari sun bukaci a mika musu barawon, amma aka ki yarda wanda hakan ya jawo tashin hankali a tsakanin al’umma.

“Wanda aka daba wa wukar yana cikin mawuyacin hali yanzu."

- Cewar wani mazaunin yankin

Matasa sun kona fadar dagaci
Wasu matasa sun cinna wuta a fadar dagaci a Katsina. Hoto: Dikko Umaru Radda.
Asali: Facebook

Asarar da aka tafka a Katsina

Wasu rahotanni sun tattabar da cewa an samu asarar dukiyoyi sanadin haka wanda ya girgiza karamar hukumar Bakori.

Sanarwar ta ce:

"Fusatattun matasa sun kona fadar Dagacin Tsiga bayan wani barawo da ya daba wa wani direban babur wuka ya nemi mafaka a can.

"Jama’a sun bukaci a mika musu barawon, amma aka ki amincewa da hakan, lamarin da ya tayar da husuma a cikin garin.
"Wanda aka daba wa wukar yanzu yana cikin mawuyacin hali a asibiti, yana samun kulawa daga likitoci domin ceton rayuwarsa.
"Garin Tsiga na karkashin karamar hukumar Bakori a jihar Katsina da ke Arewacin Najeriya."

Karanta wasu labari da suka shafi Katsina:

An kona fadar babban Sarki a Edo

A baya, mun ba ku labarin cewa wasu fusatattun matasa sun kona fadar babban basaraken jihar Edo, Olojah na Ojah, Oba Okogbe Lawani.

Lamarin ya haifar da hatsaniya da tashin hankali a tsakanin mazauna garin Ojah da ke karamar hukumar Akoko-Edo a jihar Edo da ke Kudu maso Kudancin Najeriya.

An tabbatar da cewa rikicin ya samo asali ne a yayin birne wata mata da ake zargin ta mutu a cikin gidan tsafi a yankin wanda ya ɗaga hankulan mutane.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.