El Rufai Ya Faɗi Minista 1 da Za Su Bari a Muƙaminsa bayan Sun Tura Tinubu Legas a 2027

El Rufai Ya Faɗi Minista 1 da Za Su Bari a Muƙaminsa bayan Sun Tura Tinubu Legas a 2027

  • Malam Nasir El-Rufai ya yabawa ministan sadarwa, Bosun Tijani bisa ayyuka masu kyau da yake yi domin bunƙasa harkokin fasaha
  • Tsohon gwamnan jihar Kaduna ya ce idan suka karbi mulki daga hannun Shugaba Bola Tinubu a 2027, za su bar Tijani a kan muƙaminsa
  • El-Rufai ya bayyana haka ne a wani taron fasaha da ya halarta a jihar Katsina da ke Arewa maso Yammacin Najeriya a ranar Laraba

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Katsina - Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yaba da irin ayyukan ci gaba da ministan sadarwa, kirkire-kirkire da tattalin arzikin zamani, Bosun Tijani, ke yi.

Malam El-Rufai ya bayyana cewa za su ci gaba da aiki da Bosun Tijani bayan sun tura shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya koma Legas a zaɓen 2027.

Nasir El-Rufai.
Malam Nasir El-Rufai ya yabawa ministan sadarwa, Bosun Tijani Hoto: @Elrufai
Asali: Getty Images

Tsohon gwamnan ya bayyana haka ne a wurin taron fasaha watau Arewa Tech Fest karo na biyu wanda ya gudana a jihar Katsina, kamar yadda The Cable ta kawo.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Taron, wanda ya shafe kwanaki uku, ya hada manyan masu zuba jari, ’yan kasuwa, kwararru a fannin fasaha da masana tsare-tsare, domin tattauna cigaban fasaha, musamman a Arewacin Najeriya.

Wane minista El-Rufai ya yaba da aikinsa?

Nasir El-Rufai ya ce Bosun Tijani zai ci gaba da rike mukaminsa idan haɗakar jam’iyyun adawa ta samu nasarar kayar da Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027.

Ministan sadarwa, Bosun Tijani ne ya gabatar da jawabin bude taron a Katsina, wanda Nasir El-Rufai ya halarta.

El-Rufai, wanda ya iso wurin taron a makare, ya nemi afuwa daga mahalarta, yana mai cewa rashin zuwansa da wuri ya samo asali ne daga wani muhimmin taro da suka yi a daren Talata.

"Muna shirin tura Tinubu Legas" - El-Rufai

"Dole ta sa tawagar da suka shirya taron nan suka taho suka bar ni saboda jiya Talata da daddare na halarci wani muhimmin taro na haɗaka da misalin ƙarfe 8:00 na dare.
"Taron da muka yi yana da matuƙar muhimmanci saboda muna so mu tabbatar da cewa shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya koma Legas a 2027."

- Nasir El-Rufai.

Basun Tijani.
Malam Nasir El-Rufai ya ve za su bar Bosun Tijani a minista bayan tuta Tinubu Legas Hoto: @bosuntijani @elrufai
Asali: Twitter

El-Rufai ya ce za su bar Bosun Tijani

Dangane da ministan kuma, El-Rufai ya bayyana cewa idan suka karɓi gwamnati, za su bar Bosun Tijani a kan mukaminsa saboda yana aiwatar da ayyuka masu kyau.

"Ko da mun kafa gwamnati, za mu bar Bosun Tijani a kujerarsa saboda yana yin aiki mai kyau," in ji El-Rufai.

El-Rufai na daya daga cikin jiga-jigan ’yan siyasar da ke fafutukar kafa haɗaka domin karbe mulki daga hannun APC a zaben 2027, rahoton Daily Post.

Nasir El-Rufai ya soki ɓangaren shari'a

A wani labarin kun ji cewa tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufai ya caccaki ɓangaren shari'a a Najeriya.

El-Rufai ya ce yanzu mutane sun daina yarda da shari’a a Najeriya saboda jinkirin yanke hukunci da kuma zaluntar mai gaskiya ta hanyar take masa haƙƙi.

A cewarsa, lauyoyi da alƙalai sun lalace da karɓar rashawa da harkokin rashin gaskiya, yana mai cewa lokaci ya yi da za a gyara hakan.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262