El Rufai Ya Faɗi Minista 1 da Za Su Bari a Muƙaminsa bayan Sun Tura Tinubu Legas a 2027
- Malam Nasir El-Rufai ya yabawa ministan sadarwa, Bosun Tijani bisa ayyuka masu kyau da yake yi domin bunƙasa harkokin fasaha
- Tsohon gwamnan jihar Kaduna ya ce idan suka karbi mulki daga hannun Shugaba Bola Tinubu a 2027, za su bar Tijani a kan muƙaminsa
- El-Rufai ya bayyana haka ne a wani taron fasaha da ya halarta a jihar Katsina da ke Arewa maso Yammacin Najeriya a ranar Laraba
CHECK OUT: Education is Your Right! Don’t Let Social Norms Hold You Back. Learn Online with LEGIT. Enroll Now!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Katsina - Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yaba da irin ayyukan ci gaba da ministan sadarwa, kirkire-kirkire da tattalin arzikin zamani, Bosun Tijani, ke yi.
Malam El-Rufai ya bayyana cewa za su ci gaba da aiki da Bosun Tijani bayan sun tura shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya koma Legas a zaɓen 2027.

Asali: Getty Images
Tsohon gwamnan ya bayyana haka ne a wurin taron fasaha watau Arewa Tech Fest karo na biyu wanda ya gudana a jihar Katsina, kamar yadda The Cable ta kawo.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Taron, wanda ya shafe kwanaki uku, ya hada manyan masu zuba jari, ’yan kasuwa, kwararru a fannin fasaha da masana tsare-tsare, domin tattauna cigaban fasaha, musamman a Arewacin Najeriya.
Wane minista El-Rufai ya yaba da aikinsa?
Nasir El-Rufai ya ce Bosun Tijani zai ci gaba da rike mukaminsa idan haɗakar jam’iyyun adawa ta samu nasarar kayar da Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027.
Ministan sadarwa, Bosun Tijani ne ya gabatar da jawabin bude taron a Katsina, wanda Nasir El-Rufai ya halarta.
El-Rufai, wanda ya iso wurin taron a makare, ya nemi afuwa daga mahalarta, yana mai cewa rashin zuwansa da wuri ya samo asali ne daga wani muhimmin taro da suka yi a daren Talata.
"Muna shirin tura Tinubu Legas" - El-Rufai
"Dole ta sa tawagar da suka shirya taron nan suka taho suka bar ni saboda jiya Talata da daddare na halarci wani muhimmin taro na haɗaka da misalin ƙarfe 8:00 na dare.
"Taron da muka yi yana da matuƙar muhimmanci saboda muna so mu tabbatar da cewa shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya koma Legas a 2027."
- Nasir El-Rufai.

Asali: Twitter
El-Rufai ya ce za su bar Bosun Tijani
Dangane da ministan kuma, El-Rufai ya bayyana cewa idan suka karɓi gwamnati, za su bar Bosun Tijani a kan mukaminsa saboda yana aiwatar da ayyuka masu kyau.
"Ko da mun kafa gwamnati, za mu bar Bosun Tijani a kujerarsa saboda yana yin aiki mai kyau," in ji El-Rufai.
El-Rufai na daya daga cikin jiga-jigan ’yan siyasar da ke fafutukar kafa haɗaka domin karbe mulki daga hannun APC a zaben 2027, rahoton Daily Post.
Nasir El-Rufai ya soki ɓangaren shari'a
A wani labarin kun ji cewa tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufai ya caccaki ɓangaren shari'a a Najeriya.
El-Rufai ya ce yanzu mutane sun daina yarda da shari’a a Najeriya saboda jinkirin yanke hukunci da kuma zaluntar mai gaskiya ta hanyar take masa haƙƙi.
A cewarsa, lauyoyi da alƙalai sun lalace da karɓar rashawa da harkokin rashin gaskiya, yana mai cewa lokaci ya yi da za a gyara hakan.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng