Labaran kasashen waje
Hukumar shige da fice ta Amurka ta kori 'yan Najeriya sama da 2,300 a cikin shekaru 11, inda aka sanya Najeriya a kan gaba a yawan 'yan Afirka da aka kora.
Sabuwar annobar cutar Ebola da ta bulla a DR Congo ta kashe mutane 15, WHO ta ce tana aiki cikin gaggawa tare da amfani da rigakafin Ervebo domin dakile cutar.
Shugaba Donald Trump ya karyata jita-jitar mutuwarsa da ta bazu a shafukan sada zumunta, ya ce bai taba jin wannan labarin ba sai da aka tambaye shi.
An hallaka tsohon kakakin majalisar dokokin Ukraine, Andriy Parubiy, a Lviv, abin da ya tayar da hankula a kasar, yayin da shugabanni ke aika wa da sakon ta’aziyya.
Rahotanni daga kasar Mexico sun nuna cewabsanatoci su ba hammata iska a zaman ranar Laraba, inda lamarin ya kai ga doke doke da ture-ture a zauren Majalisa.
Kotun Equatorial Guinea ta yanke wa Ruslan Obiang Nsue, dan shugaban kasa, hukuncin shekara shida bayan samunsa da laifin sayar da jirgin gwamnatin kasar.
Wata kotu a kasar Equatorial Guinea ta hukunta Balthazar Engonga Ebang, bayan ta same shi da laifi kan tuhume-tuhumen da suka shafi almundahanar kudade.
NNPCL ya ce ya gano cewa akwai kungiyoyin kasashen waje da ke da hannu a satar man Najeriya, yana mai cewa haɗin kai da hukumomin tsaro, ya sa samar da mai ya karu.
Isra’ila ta kai hari wani asibitin Gaza inda aka kashe mutane 15 ciki har da ‘yan jarida, Hamas ta ce shirin Isra’ila na kwace Gaza barazana ce ga zaman lafiya.
Labaran kasashen waje
Samu kari