Zaben Najeriya
Jam'iyya mai mulki ta APC tana samun tagomashin sababbin yan siyasa da suka yi fice a jam'iyyusu na PDP, NNPP da LP, kuma ana sa ran wasu za su sauya sheka nan gaba.
Hukumar zabe ta INEC na son kawo sauyi a dokar zabe domin ba marasa katin PVC damar kada kuri'a a zaben 2027. Hakan zai rage kudin da INEC ke kashewa.
Tsohon gwamnan Delta kuma mataimakin Atiku Abubakar a takarar zaben 2023, Ifeanyi Okowa da wasu jiga-jigan PDP sun koma jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya.
Shugaban APC, Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana cewa kalaman Buba Galadima na cewa ba shi da amfani a siyasa, shaci fadi ne kawai, domin an san muhimmancinsa.
Jigo a APC kuma tsohon sakataren gwamnatin Muhammadu Buhari,Babachir Lawal ya bayyana takaicin salon mulkin APC a karkashin Bola Ahmed Tinubu a kasar nan.
Tsohon hadimin mataimakin shugaban ƙasa wanda ya ajiye aiki, Dr. Hakeem Baba Ahmed ya ce dole ne a yi tsayin daka wajen zaɓen nagartaccen ɗan takara a 2027.
Wasu rahotanni sun ce akwai gwamnoni uku ko hudu da ke PDP na shirin sauya sheka zuwa APC, domin marawa shugaba Tinubu baya a yunkurinsa na zarce a 2027.
Yayin da zaben 2027 ke karatowa, an ce tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar na shirin takara a 2027 tare da Peter Obi a matsayin mataimakinsa.
Sanata Barau I Jibrin ya bayyana cewa 'yan Najeriya sun aganin irin ayyukan alheri da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta ke aiwatarwa duk da matsaloli a duniya.
Zaben Najeriya
Samu kari