Zaben Najeriya
Tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya ce idan kotuna za su fara adalci ga 'yan siyasa kashi 50% na 'yan siyasa za su daina shigar da kara idan sun fadi zabe.
Bincike ya fallasa yadda gwamnatocin jihohin kasar nan 30 suka kashe makudan kudi wajen sayen kayan kwalam da makulashe da walwalar jami'an zaman gwamnati.
Tsohon mai binciken kudi na APC na kasa, Sir Paul Chukwuma, ya bayyana cewa zai kayar da Gwamna Charles Soludo idan ya lashe tikitin takarar gwamna na APC a 2025.
Kungiyar SERAP ta bukaci Shugaba Bola Tinubu da ya yi amfani da bikin cika shekara daya a kan karagar mulki wajen bayyana yawan kadarorin da ya mallaka.
Kungiyar matasan APC na kasa sun barranta kansu da masu fafutukar tsige shugaban jam'iyyar na Kasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje daga shugabancin jam'iyyar.
Kungiyar Kabilar Ibo ta Ohanaeze ta gargadi tsohon dan takarar shugaban kasa a zaben da ya gabata karkashin ya yi hankali da 'yan Arewa a zaben 2027.
Tsohon gwamnan jihar Katsina, Aminu Masari ya ce wadanda ke nadamar zaben Tinubu a 2023 suna hankoro ne saboda ba su samu abinda suke so ba a gwamnatin.
Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabun Garki da Babura, Isa Dogonyaro, daga jihar Jigawa ya rasu a Abuja. Iyalan marigayin sun tabbatar da rasuar yau Jumu'ah.
Shahararren masanin tattalin arzikin siyasa a Najeriya, Farfesa Pat Utomi ya ce ana gagarumin shirin hadakar adawa mai karfi a zaben 2027 mai zuwa.
Zaben Najeriya
Samu kari