Kasar China ta fitar gda gargadi bayan wani hari da Amurka ta kai tare da kwace jirgin Iran a teku. Lamarin ya sanya China cewa hakan zai dagula sulhun da ake son yi
Kasar China ta fitar gda gargadi bayan wani hari da Amurka ta kai tare da kwace jirgin Iran a teku. Lamarin ya sanya China cewa hakan zai dagula sulhun da ake son yi
Gwamnatocin Najeriya da Turkiyya za su kafa cibiyar horas da sojoji a Najeriya domin taimakon kasar ta magance matsalar tsaro da ta yi katutu a Najeriya.
Wani mutumi ya ce ga garin ku nan bayan ya gama sheke ayarsa da wata mata a otal. Rundunar yan sandan jihar ta cafke mutum biyu da ake zargi da hannunsu a lamarin.
Wani sojan baka a siyasar Kano, Dan Bilki Kwamanda, ya ce nan ba da dadewa ba za su kawo karshen siyasar jagoran NNPP, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso..
Jami'ar Bayero da ke Kano ta musanta rahoton da ake yaɗawa cewa an yi garkuwa da mutane a harabar jami'ar da ke cikin birnin Kano, ta ce labarin kanzon kurege ne.
Shugaba Bola Tinubu ya bukaci kungiyar CAN da ta taimaka wajen yakar cin hanci da rashawa ta hanyar yin wa’azin hakuri da juriya don yan Najeriya su sauya tunaninsu.
Shahararriyar jarumar fina-finan kudu wato Nollywood, Destiny Etiko ta bayyana cewa idan har Allah zai sake hallito ta a wata rayuwar a baturiya take son fitowa.
Bayo Omoboriowo, tsohon mai daukar hoton tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tuna yadda ya yi aiki a fadar shugaban kasa dake babban birnin Abuja.
Wasu miyagun yan bindiga sun kai sabon farmaki a jihar Ƙaduna. Miyagun yan bindigan a yayin farmakin sun yi awon gaba da wasu mutum hudu yan gida daya.
Rundunar 'yan sanda ta kama Mansir Hassan, wanda ke yi wa 'yan ta'adda safarar makamai a dajin Zurmi, jihar Zamfara. An kama shi ne a yankin Zariya a kan babur.
Sakataren harkokin kasar Amurka, Anthony Blinken, ya iso Najeriya inda zai gana da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu. Blinken zai kuma gana da yan kasuwa.
Labarai
Samu kari