Ya Halasta Ga Musulmai Ma’aurata Su Yi Jima’i a Cikin Watan Ramadana da Dare

Ya Halasta Ga Musulmai Ma’aurata Su Yi Jima’i a Cikin Watan Ramadana da Dare

  • Malamin addinin Islama ya bayyana kadan daga abin da ya kamata Musulmai su mai da hankali a kai tsakaninsu da abokan zamansu a azumi
  • Malamin ya ce, ya halasta Musulmi ya kusanci matarsa a watan Ramadana, amma a wani kebabben lokaci
  • Musulmai a duniya na azumin watan Ramadana, daya daga cika-cikan addinin mafi yawan fadada a duniya

Abeokuta, jihar Ogun - Limamin masallacin jami’ar noma ta tarayya da ke Abeokuta, Farfesa Sherifdeen Kareem ya ce, ya halasta ma’aurata Musulmai su yi saduwar aure a cikin watan Ramadana.

Ya bayyana cewa, hakan zai yiwu ne kadai daga bayan buda-baki har zuwa cikin dare, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

A cewar malamin a lokacin da yake zantawa da jaridar, ya haramta ga Musulmai maza da mata su yi zina a cikin watan Ramadana ko wajensa.

Kara karanta wannan

Wajibi ne Idan Tinubu Ya Hau Mulki, Ya Karawa Ma’aikata Albashi – Ministan Buhari

Ya halasta a yi jima'i a Ramadana, inji malamin addini
Musulmai na sallah a masallacin idi | Hoto: Hoto: dailypost.ng
Asali: UGC

Lokacin da ya halasta ma’aurata su kusanci juna

Ya kara dacewa, addinin Islama ne kadai ya ba Musulmai ma’aurata ‘yancin yin jima’i daga sallar bayan Magriba zuwa ketowar Al-fijir a lokacin azumi.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

A kalamansa:

“Musulmai za su iya saduwar aure a lokacin da suka yi buda-baki, kenan bayan sallar Magriba. Matukar dai za su ci abinci, to ya halasta su taki junansu har zuwa ketowar Al-fijir.
“An ba maza damar jima’i da matansa ko mata da mazajensu daidai da ‘yancin cin abinci da shan ruwa.
“Wannan a kebe yake ga maza ma’aurata. Idan basu da aure, zina haramun ne a kowane lokaci. Don haka, addinin islama ne kadai ya ba ma’urata ‘yancin yin jima’i a azumi, tsakanin Magriba da Asuba.”

A dan nesanci juna idan ana azumi

A bangare guda, malamin ya shawarci ma’aurata Musulmai da su nesanci juna da rana idan suna azumi don gudun fitina.

Kara karanta wannan

To fah: Mataimakin shugaban APC ya fadi yankin da ya kamata a ba kujerar Ahmad Lawal

A cewarsa, Annabi Muhammadu (SAW) ya sumbaci matarsa a cikin watan Ramadana, amma duk da haka ya shawarci Musulmai da su nesanci junansu da rana saboda komai zai iya faruwa.

A wannan watan na Ramadana ne Musulmai a duniya ke azumtar kwanaki 29 ko 30 a matsayin daya daga cika-cikan Musulunci.

Kira ga masu zuwa ziyarar Hajji da Umrah

A wani labarin, kasar Saudiyya ta bayyana kira ga Musulmai masu zuwa ziyara da su guji yawaita daukar hotuna a lokacin ibada.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Musulmai ke shagala da yawan dauke-dauke hotunan a ziyarar Hajji da Umrah.

Saudiyya ta ce, ya kamata Musulmai su zama masu mutunta masallatan Harami guda biyu tare da gudun aikata ‘Riya’.

Asali: Legit.ng

Online view pixel