Ya Halasta Ga Musulmai Ma’aurata Su Yi Jima’i a Cikin Watan Ramadana da Dare
- Malamin addinin Islama ya bayyana kadan daga abin da ya kamata Musulmai su mai da hankali a kai tsakaninsu da abokan zamansu a azumi
- Malamin ya ce, ya halasta Musulmi ya kusanci matarsa a watan Ramadana, amma a wani kebabben lokaci
- Musulmai a duniya na azumin watan Ramadana, daya daga cika-cikan addinin mafi yawan fadada a duniya
Abeokuta, jihar Ogun - Limamin masallacin jami’ar noma ta tarayya da ke Abeokuta, Farfesa Sherifdeen Kareem ya ce, ya halasta ma’aurata Musulmai su yi saduwar aure a cikin watan Ramadana.
Ya bayyana cewa, hakan zai yiwu ne kadai daga bayan buda-baki har zuwa cikin dare, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
A cewar malamin a lokacin da yake zantawa da jaridar, ya haramta ga Musulmai maza da mata su yi zina a cikin watan Ramadana ko wajensa.

Kara karanta wannan
Wajibi ne Idan Tinubu Ya Hau Mulki, Ya Karawa Ma’aikata Albashi – Ministan Buhari

Asali: UGC
Lokacin da ya halasta ma’aurata su kusanci juna
Ya kara dacewa, addinin Islama ne kadai ya ba Musulmai ma’aurata ‘yancin yin jima’i daga sallar bayan Magriba zuwa ketowar Al-fijir a lokacin azumi.
DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka
A kalamansa:
“Musulmai za su iya saduwar aure a lokacin da suka yi buda-baki, kenan bayan sallar Magriba. Matukar dai za su ci abinci, to ya halasta su taki junansu har zuwa ketowar Al-fijir.
“An ba maza damar jima’i da matansa ko mata da mazajensu daidai da ‘yancin cin abinci da shan ruwa.
“Wannan a kebe yake ga maza ma’aurata. Idan basu da aure, zina haramun ne a kowane lokaci. Don haka, addinin islama ne kadai ya ba ma’urata ‘yancin yin jima’i a azumi, tsakanin Magriba da Asuba.”
A dan nesanci juna idan ana azumi
A bangare guda, malamin ya shawarci ma’aurata Musulmai da su nesanci juna da rana idan suna azumi don gudun fitina.

Kara karanta wannan
To fah: Mataimakin shugaban APC ya fadi yankin da ya kamata a ba kujerar Ahmad Lawal
A cewarsa, Annabi Muhammadu (SAW) ya sumbaci matarsa a cikin watan Ramadana, amma duk da haka ya shawarci Musulmai da su nesanci junansu da rana saboda komai zai iya faruwa.
A wannan watan na Ramadana ne Musulmai a duniya ke azumtar kwanaki 29 ko 30 a matsayin daya daga cika-cikan Musulunci.
Kira ga masu zuwa ziyarar Hajji da Umrah
A wani labarin, kasar Saudiyya ta bayyana kira ga Musulmai masu zuwa ziyara da su guji yawaita daukar hotuna a lokacin ibada.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Musulmai ke shagala da yawan dauke-dauke hotunan a ziyarar Hajji da Umrah.
Saudiyya ta ce, ya kamata Musulmai su zama masu mutunta masallatan Harami guda biyu tare da gudun aikata ‘Riya’.
Asali: Legit.ng