Latest
Tsohon babban lauyan gwamnatin tarayya kuma tsohon Ministan tarayya, Abubakar Malami, ya shiga takarar gwamnan jihar Kebbi a inuwar jam'iyyar ADC.
Dakarun Operation Fansan Yamma sun kama wani da ake zargin dan bindiga ne a Birnin Gwari tare da kwato mujallar bindigar AK-47, wayoyi da tabar wiwi.
Sanata mai wakiltar Gombe ta Kudu, Anthony Siyako, ya sauya sheka zuwa jam'iyyar PDP mai adawa. Sanatan ya koma PDP ne bayan rasa tikitin jam'iyyar APC.
Gwamnan Rivers, Siminalayi Fubara, bai halarci tantancewar APC ba yayin da jam’iyyar ta tantance gwamnoni 14 da sauran masu neman mukaman zaben 2027.
Rundunar IRGC ta Iran ta yi barazanar kai munanan hare-hare kan sansanonin Amurka da jiragen ruwa idan aka kai hari kan tankokin mai ko jiragen kasuwancin Iran.
A labarin nan, za a ji cewa kungiyar Kwankwasiyya ta bayyana yakinin cewa za ta kauce wa matsalolin da aka samu a ADC a cikin sabuwar jam'iyyar NDC.
Rabiu Kwankwaso ya goyi bayan matakin jam’iyyar NDC na bai wa Kudancin Najeriya tikitin takarar shugaban ƙasa na 2027 domin kammala tsarin karɓa-karɓa na shugabanci.
Daliban da suka ci gajiyar shirin NELFUND a Anambra sun bayyana goyon baya ga shugaba Bola Tinubu domin ya sake tsayawa takarar shugaban kasa a 2027.
Mutum 6 daga cikin wadanda suka nuna sha'awar takarar gwamnan jihar Yobe a Inuwar APC sun garzaya sun gana da mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima.
Masu zafi
Samu kari