Kwankwaso da Wasu Gwamnonin Najeriya da Suka Taba Mikawa Mataimakansu Mulki

Kwankwaso da Wasu Gwamnonin Najeriya da Suka Taba Mikawa Mataimakansu Mulki

Kano - A siyasar Najeriya, dangantaka tsakanin gwamna da mataimakinsa tamkar wasan kwaikwayo ce mai cike da sarkakiya; wasan ne da ke bukatar biyayya, ɓoye buri, da kuma nuna dabarun neman mulki a taka tsan-tsan.

Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Mataimakan gwamnoni da dama sukan zauna a innuwar iyayen gidansu, suna kwantar da kai matsayin amintaccen bawa da ke jiran ranar da za a ba shi ragamar masarauta.

An samu gwamnonin Najeriya da suka goyi bayan mataimakansu suka zama gwamna.
Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, da Mohammed Badaru Abubakar. Hoto: @KwankwasoRM, @Mohammed_Badaru
Source: Twitter

Mataimaka da dama suna share shekaru takwas suna biyayya da fatan idan lokacin da wa'adin maigidansu ya zo kare wa, zai naɗa su a matsayin magada, in ji rahoton Leadership.

Yayin da amincewa da goyon baya daga gwamna kan iya zama silar nasara ga mataimakansu, a hannu daya kuma, goyon bayan na iya zama silar shan kaye mai raɗaɗi a ranar zaɓe.

Kara karanta wannan

Sanata kwankwaso ya fito da bayanai game da dalilansu na barin ADC

Gwamnonin da suka goyi bayan mataimakansu

A wannan rahoto, Legit Hausa ta jero wasu gwamnonin Najeriya da suka goyi bayan mataimakansu suka zama gwamnoni, da wadanda goyon bayansu bai yi tasiri ba a rumfar zaɓe:

1. Rabiu Musa Kwankwaso (Kano)

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya mika mulki ga mataimakinsa Abdullahi Ganduje a zaben 2015.
Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da Abdullahi Umar Ganduje. Hoto: @KwankwasoRM
Source: Twitter

Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya tsaya tsayin daka wajen ganin mataimakinsa, Abdullahi Umar Ganduje, ya gaje shi a zaɓen 2015.

Kwankwaso ya yi amfani da dukkan ƙarfinsa da tasirin jam’iyyar APC na wancan lokacin wajen ba wa Ganduje damar samun nasara.

A zaɓen 2015, Ganduje ya doke babban ɗan takarar PDP, Salihu Sagir Takai, bayan ya samu ƙuri'u 1,546,434 yayin da shi Takai ya samu kuri'u 509,726 kamar yadda Channels TV ta ruwaito.

Duk da irin wannan kauna da ke tsakaninsu, baraka ta zo ta shiga tsakanin Kwankwaso da Ganduje, lamarin da ya sa suka koma abokan gaba.

2. Ahmad Sani Yerima (Zamfara)

Gwamna Ahmad Sani Yerima ya taimaka wa mataimakinsa MAhmud Shinkafi ya zama gwamna a 2007
Hagu zuwa dama: Ahmad Sani Yerima, Mahmud Shinkafi, Dauda Lawal, Abdulaziz Yari, Bello Matawalle. Hoto:@Bellomatawalle1
Source: Twitter

Idan ana maganar goyon bayan mataimaki har ya ci zabe cikin lumana, to ba za a manta da Jihar Zamfara ba, inda Gwamna Ahmad Sani Yerima (1999–2007) ya goyi bayan mataimakinsa, Mahmud Aliyu Shinkafi ya lashe zaben gwamna.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Kano ta musanta kashe mutane bayan nada Murtala Garo, ta soki Amnesty

Da taimakon ikon gwamnati da na jam’iyyar ANPP, Shinkafi ya lashe zaɓen 2007 ba tare da ya sha wata wahala ba, in ji rahoton Daily Trust.

Shinkafi ya mulki Zamfara na tsawon shekaru huɗu, kodayake daga baya ya sauya sheƙa zuwa jam'iyyar PDP, matakin da aka yi zargin ya kawo karshen zumuncin siyasarsa da Yerima.

3. Mohammed Badaru Abubakar (Jigawa)

Mohammed Badaru Abubakar ya taka rawar gani wajen ganin mataimakinsa Umar Namadi ya lashe zaben gwamnan Jigawa a 2023.
Umar Namadi, gwamnan Zamfara, da Mohammed Badaru Abubakar, tsohon ministan tsaro. Hoto: @MODInfoNg
Source: Twitter

A jihar Jigawa ma, tsohon gwamna Mohammed Badaru Abubakar ya ba da mamaki wajen marawa mataimakinsa, Umar Namadi, baya a zaɓen 2023.

Tun farko, Namadi mutumin Badaru ne tun yana kwamishinan kuɗi, sannan ya zama mataimakinsa a 2019.

Saboda amincin da ke tsakaninsu, Namadi ya sami tikitin APC cikin sauƙi kuma ya lashe zaɓen gwamna da gagarumin rinjaye, inda ya samu kuri'u 618,449, cewar rahoton Premium Times.

4. Abdullahi Umar Ganduje (Kano)

A 2023, Abdullahi Umar Ganduje ya so mataimakinsa, Nasiru Gawuna ya gaje ji, amma ya sha kasa a hannun Abba Yusuf.
Abdullahi Umar Ganduje da tsohon gwamnan Kano, Nasiru Gawuna. Hoto: @Gawuna2023
Source: Twitter

Kaddara ta juya wa Ganduje baya lokacin da ya so ya kwaikwayi abin da Kwankwaso ya yi masa. Shi ma ya tsayar da mataimakinsa, Nasiru Yusuf Gawuna, domin ya gaje shi a zaɓen 2023.

Duk da iko da kuɗin da aka ce Ganduje ya narka a takarar Gawuna, hakan bai kai shi ga gaci ba, ya sha kaye a hannun ɗan takarar NNPP, Abba Kabir Yusuf, da tazarar ƙuri'u da suka haura 100,000.

Kara karanta wannan

Jerin gwamnonin Arewa da suka fitar da wadanda za su gaje su a zaben 2027

Kodayake an tafi kotu har zuwa matakin ƙarshe, Kotun Ƙoli ta tabbatar da cewa Abba Kabir ne halastaccen gwamnan Kano, in ji rahoton ICRI.

5. Babajide Sanwo-Olu (Legas)

Gwamnan Legas, Babajide Sanwo-Olu ya tsayar da mataimakinsa Dr. Obafemi Hamzat matsayin dan takarar gwamna
Gwamnan Legas, Babajide Sanwo-Olu tare da mataimakinsa Dr. Obafemi Hamzat. Hoto: jidesanwoolu
Source: Twitter

Yanzu idanu sun koma jihar Legas, inda Gwamna Babajide Sanwo-Olu ya riga ya zaɓi mataimakinsa, Dr. Obafemi Hamzat, a matsayin magajinsa a 2027.

Wannan sanarwa da aka yi a watan Afrilun 2026 ta sami babban goyon baya daga manyan iyayen jam'iyyar, ciki har da Shugaba Bola Tinubu, in ji rahoton Vanguard.

Sanwo-Olu ya bayyana cewa Hamzat mutum ne mai ilimi da sanin aiki, kuma ya cancanci ya jagoranci Legas. Tuni dai ƙungiyoyi daban-daban a jihar suka fara gangamin ganin cewa wannan buri ya tabbata.

Rikici tsakanin gwamnoni da mataimakansu

A wani labari, mun ruwaito cewa, rikicin siyasa tsakanin wasu gwamnoni da mataimakansu na barazana game ci gaba da kasancewarsu zuwa zaben 2027.

A jihohi kamar Niger da Taraba, matsaloli irin su rikici tsakanin shugabanni da rashin lafiya na iya hana mataimakan gwamnoni tsayawa.

Duk da kyakkyawar alaka a Plateau, shekarun mataimakiyar gwamna Josephine Piyo na iya hana ta ci gaba da takara mai zuwa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com