Rikicin PDP
Shugaban PDP, Umar Damagum ta bayyana cewa 'yan Najeriya ne ke rike da ikon zaben wanda zai ci gaba da jagorancinsu a babban zaben 2027 mai karato wa.
Ƙungiyar PDP 100 Percent ta bukaci Atiku Abubakar da ya hakura da takara a 2027, ta nemi jam’iyyar ta mara wa ɗan takarar Kudu baya don adalci da hadin kai.
Tsohon dan majalisa wakilan kasar nan, Tajudeen Yusuf ya ce wasu gwamnoni a jam'iyyar PDP na haddasa rikici don su samu hujjar sauya sheka zuwa APC.
Hadakar Atiku ta ce sauya shekar gwamnonin PDP ba abin mamaki ba ne, tana zargin wasu da yin aiki da Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu kafin 2027.
Usman Bugaje ya ce jam'iyyar APC na amfani da kuɗi da barazana wajen janyo ‘yan adawa, yana mai cewa hakan na rushe siyasa da dimokuraɗiyyar Najeriya.
Gwamnan jihar Delta, Sheriff Obovrevwori, ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC a ranar Laraba, sakamakon rikici da ya mamaye PDP da wasu matsalolin siyasa a jihar.
Magoya bayan Wike a PDP sun kafa sababbin shugabanni a Edo da Bayelsa, inda ake zargin rikicin fidda gwani da gangamin Bayelsa ne suka jawo wannan barakar.
Yarjejeniyar sirri da ake zargin an kulla tsakanin Tinubu da gwamnoni na PDP na ƙara rura rikicin shugabanci a jam'iyyar, yayin da Tinubu ke neman tazarce a 2027.
Tsohon gwamnan Delta kuma mataimakin Atiku Abubakar a takarar zaben 2023, Ifeanyi Okowa da wasu jiga-jigan PDP sun koma jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya.
Rikicin PDP
Samu kari