NiMet: Ana Hasashen Ruwan Sama Zai Sauka a Abuja da Jihohin Arewa 5 Ranar Juma'a

NiMet: Ana Hasashen Ruwan Sama Zai Sauka a Abuja da Jihohin Arewa 5 Ranar Juma'a

  • Hukumar NiMet ta sanar da cewa za a samu yanayin zafi da rana a Arewa, yayin da za a yi ruwan sama a mafi yawancin jihohin Kudu
  • Ana sa ran samun guguwa da iska mai karfi kafin fara ruwan sama, wanda hakan na iya haddasa hadari a tituna da kuma gidaje
  • Yayin da NiMet ta jero jihohin Arewa biyar da za su iya samun ruwan sama a ranar Juma'a, hukumar ta gargadi direbobin da ke tuki ana ruwa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Abuja – Hukumar hasashen yanayi ta kasa (NiMet) ta fitar da jadawalin yanayin da za a fuskanta a fadin kasar nan ranar Juma'a, 24 ga watan Afrilu, 2026.

NiMet ta bayyana cewa za a samu sauyin yanayi daga zafi zuwa ruwan sama a sassa daban-daban, yayin da wasu jihohin za su fuskanci zafi kawai.

Kara karanta wannan

Laraba: Rana za ta yi zafi sosai a Arewa, za a samu ruwan sama a Neja da jihohi 7

NiMet ta yi hasashen saukar ruwan sama a Abuja da wasu jihohin Najeriya ranar Juma'a.
Iska mai karfi na kadawa yayin da ake ruwan sama. Hoto: Sani Hamza/Staff
Source: Original

Hukumar ta fitar da hasashen yanayin na ranar Juma'a ne a cikin sanarwar da ta fitar a shafinta na X a daren Alhamis, 23 ga Afrilu, 2026.

Hasashen yanayi a jihohin Arewa

A Arewa maso Yamma da maso Gabas, NiMet ta ce za a wayi gari da yanayin rana mai zafi a mafi yawancin jihohin shiyyoyin biyu.

Sai dai akwai yiwuwar samun tsawa da walkiya a wasu sassa na jihar Adamawa tun da safe. Daga baya kuma za a iya samun matsakaicin ruwan sama a Adamawa da Taraba.

A Arewa maso tsakiyar Najeriya, za a samu haduwar hadari a sararin samaniya, amma rana za ta hudo, ta kuma shiga cikin giza gizai lokaci zuwa lokaci.

Idan yamma ta yi, ana sa ran samun ruwan sama da tsawa a babban birnin tarayya Abuja da jihohin Benue, Kogi, Kwara.

Hasashen yanayi a Kudancin Najeriya

Kara karanta wannan

Sojan Isra'ila ya yi wulakanci mai muni ga Yesu Almasihu, an fara sukar kasar

Hasashen NiMet ya kuma nuna cewa za a samu saukar ruwan sama a mafi yawan jihohin da ke a shiyyar Kudancin Najeriya.

Sai dai, NiMet ta ce za a fara samun ruwan a Akwa Ibom da Cross River tun da safe. Amma idan yamma ta yi, ruwan zai sauka a jihohin Legas, Ogun, Edo da Delta.

Sauran jihohin da za su samu ruwan sama hade da tsawa sun hada da Bayelsa, Rivers, Abia, Imo, Anambra, Enugu da Ebonyi.

Ana fargabar cewa wannan mamakon ruwa da zai sauka zai iya haddasa ambaliya a sassa daban daban na Kudancin kasar.

NiMet ta yi hasashen cewa ruwan sama zai sauka a Abuja da jihohi 5 na Arewa.
Yara na wasa yayin da ake ruwa a garin Nafada, jihar Gombe. Hoto: Jamsy El-nfaty
Source: Facebook

NiMet ta bada muhimman shawarwari

Hukumar ta fitar da wasu shawarwari domin kare kai daga hatsari:

  • Mutane su yi hattara domin za a iya samun iska mai karfi; an bukaci mutane su killace abubuwan da iska kan iya dauka.
  • An bukaci direbobi su rage gudu yayin da ake ruwa domin hanya tana santsi kuma gani yana raguwa.
  • Mutane su guji bi ta hanyoyin da ruwa ke taruwa ko ya saba yin ambaliya.
  • Idan ana walkiya, an bukaci mutane su nemi wurin buya domin kauce wa saukar tsawa..

Kara karanta wannan

An kama gungun barayin mai da suka nufi matatar Dangote a Legas

Duba hasashen yanayin a kasa:

An bada mafita kan ambaliya a Arewa

A wani labari, mun ruwaito cewa, dattawan Arewa sun bukaci gwamnatoci da mutanen da ke zaune a yankunan da ambaliya ke yawan faruwa da su dauki matakan kariya.

ACF ta nuna damuwa kan hasashen da NIHSA ta fitar, wacce ta ce akalla garuruwa 1,249 a kananan hukumomi 176 na jihohi 30 da Abuja na fuskantar barazanar ambaliya.

Dattawan Arewa sun kuma bukaci hukumomin agaji su tanadi abinci, magunguna, ruwa da sauran kayan bukatu don tallafawa wadanda za su iya fuskantar ambaliya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com