Manyan Labarai A Yau
Jam'iyyar PDP mai adawa a Najeriya ta yi babban rashi a jihar Sokoto bayan ficewar wani babban jigo a cikinta. Sanata Abdallah Wali ya raba gari da PDP.
Kungiyar kwallon kafa ta Manchester United da ke kasar Ingila ta raba gari da mai horar da manyan 'yan wasanta, Ruben Amorim bayan ya yi kunnen doki da Leeds.
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasa (EFCC), ta yi magana kan shari'ar tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello. Ta ce lamarin yana gaban kotu.
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ci gaba da shirye-shiryen komawa jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya. An ji mutanen da za su bi shi daga NNPP.
An binne tsohon Kwamishinan Ilimi na jihar Kaduna, Alhaji Suleiman Lawal Kauru, a Zaria bayan ya rasu yana da shekaru 78 a asibitin koyarwa na ABUTH da ke Shika.
Yara 11 sun tsinci harsasan kakkabo jiragen sama a magudanar ruwa a Maiduguri; sojoji sun killace yankin yayin da aka bai wa yaran kyautar kuɗi saboda jarumta.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya fusata kan harin da 'yan ta'adda suka kai a wata kasuwa da ke jihar Neja. Ya umarci jami'an tsaro su farauto tsagerun.
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya dage lokacin da ya shirya komawa jam'iyyar APC. Gwamnan ya dage lokacin ne domin ci gaba da wasu shirye-shirye.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu gagarumar nasara bayan sun farmaki 'yan bindiga a kan iyakokin Katsina da Kano. Sojojin sun hallaka 'yan bindiga da dama.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari