Manyan Labarai A Yau
Shugaban jam'iyyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya mika kokon bararsa ga attajiran jihar Anambra. Ganduje ya bukaci su gina jam'iyyar APC.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya ki amincewa da dokar da za ta kafa sabuwar jami'ar gwamnatin tarayya a jihar Adamawa. Ya ce akwai kura-kurai a ciki.
Rundunar ƴan sandan jihar Ogun ta gurfanar da wani dattijo a gabam kuliya kan tuhumar haɗin kai, cin zarafin wani bawan Allah, kotu ta ɗage zaman.
Babbar kotun jihar Kogi mai zama a birnin Lokoja ta ce an saɓawa doka da ka'idojin sarautar gargajiya wajen naɗin sarkin kasar Ebira, mai martaba Ahmed Anaje.
Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja, ta ba da umarnin a tsare tsohon shugaban hukumar NHIS, Farfesa Usman Yusuf a gidan gyaran hali na Kuje.
Rahotanni sun nuna cewa jami'an tsaro sun harbe wasu mutane yayin rusau a jihar Kano. Mutanen dai sun rasa rayukansu ne bayan sun ki amincewa a rushe gidajensu.
Wasu 'yan bindiga dauke da makamai sun kai harin ta'addanci a jihar Taraba. 'Yan bindigan sun kashe mutum daya tare da yin garkuwa da wasu mutane daban.
Jami'an tsaro na 'yan sanda da sojoji sun samu nasarar ceto wasu mutane da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su a jihar Kaduna. Sun sada su da iyalansu.
Gwamnatin tarayya ta shirya gudanar da taro da kungiyar kwadago ta kasa (NLC) kan karin kudin kira da data. NLC dai ta shirya gudanar da zanga zanga kan karin.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari