Salihu Lukman: Tsohon Shugaba a APC Ya Sake Dura kan Gwamnatin Bola Tinubu
- Tsohon mataimakin shugaban APC na ƙasa, Salihu Lukman, ya nuna rashin gamsuwarsa da kamun ludayin Bola Tinubu
- Salihu Lukman ya ƙalubalanci gwamnatin kan rashin samar da wani ingantaccen tsarin tattalin arziƙi da zai amfani ƴan Najeriya
- Tsohon jigon na APC na Arewacin kasar nan ya ce ya cire tsammanin cewa gwamnatin Tinubu za ta taɓuka wani abin kirki
CHECK OUT: Education is Your Right! Don’t Let Social Norms Hold You Back. Learn Online with LEGIT. Enroll Now!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
FCT, Abuja - Tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Salihu Lukman, ya caccaki gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.
Salihu Lukman ya bayyana cewa gwamnatin Shugaba Tinubu ba ta da wani ingantaccen tsarin tattalin arziƙi da zai amfani ƙasar nan.

Asali: Twitter
Salihu Lukman ya bayyana hakan ne yayin wata hira da tashar Channels tv a shirinsu na 'Inside Sources'.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Salihu Lukman ya caccaki Bola Tinubu
Tsohon mataimakin shugaban na APC ya kuma ya bayyana rashin jin daɗinsa game da salon shugabancin Tinubu.
Ya soki dalilin da ya sa shugaban ƙasa ya cire tallafin fetur da kuma sakin Naira sakaka ba tare da wani ingantaccen shiri na bunkasa masana’antu da ƙarfafa samun kuɗin shiga ga ƴan ƙasa ba.
Salihu Lukman ya kuma ce Tinubu ya ware kansa domin bai bari ana ganinsa.
"Kamar ya ware kansa ne, har a cikin jam’iyya ma. Babu wanda ke sauƙin samun ganinsa, kuma wannan ba irin shugabancin ci gaba bane da nake zato zai yi."
- Salihu Lukman
Ya bayyana cewa salon mulkin Tinubu ya sha banban da irin yadda ya tafiyar da gwamnatinsa lokacin da ya kasance gwamnan Legas.
"A ra’ayina, ba haka ya tafiyar da jihar Legas ba. Na kai ga yanke shawarar cewa ba zan iya sa ran wani abin kirki zai fito daga wannan gwamnati ba."
"Na gama yanke shawarar cewa babu wani abin kirki da zai fito, kuma saboda haka dole ne mu fara shiri."
"Na faɗi haka tun da farko, wannan ƙasa za a iya gyarata a zamaninmu, kuma ina roƙon Allah Ya ba mu ƙarfin hali da ƙwarin gwiwa mu fuskanci shugabanninmu.”
- Salihu Lukman

Asali: Twitter
Meyasa Salihu ya daina goyon bayan Tinubu?
Salihu Lukman ya ce ya jira har zuwa watan Yuli na bara kafin ya janye goyon bayansa ga Tinubu, yana mai cewa shugaban ƙasar ya killace kansa, har da ƴan jam’iyyarsa, domin babu wanda ke samun damar ganinsa.
Ya ƙara da cewa kafin faruwar hakan yana da tabbacin cewa Tinubu zai gyara kura-kuren da Muhammadu Buhari ya yi.
'Dan siyasar ya ce rashin nasarar Tinubu yanzu ta sa Buhari yana kama da gwarzo a idon jama'a.
Salihu Lukman ya faɗi kuskuren El-Rufai
A wani labarin kuma, kun ji cewa tsohon mataimakin shugaban jam'iyyar APC na ƙasa, Salihu Lukman, ya ce Nasir El-Rufai ya yi saurin sauya sheƙa bayan yaAPC
Salihu Lukman an ya bayyana cewa komawar tsohon gwamnan Kaduna zuwa jam'iyyar SDP, abu ne wanda ya yi cikin sauri.
Ya nuna cewa ficewarsa daga APC zuwa SDP na iya kawo cikas ga tattaunawar da ƴan adawa suke yi domin kafa haɗaka.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng