Manyan Labarai A Yau
Hukumar Hisbah ta cafke wasu matasa da ake zargi da rashin yin azumi a ranar farko ta watan Ramadan. Jami'an hukumar sun kuma kama masu askin banza.
Wata coci a jihar Kaduna ta tuna da al'ummar musulmai yayin da suka fara azumin watan Ramadan. Cocin ta raba kayayyakin abinci ga mutane mabukata.
Shugaban jam'iyyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya aika da sakon taya al'ummar musulmi murnar shigowar watan Ramadan. Ya bukaci a dage wajen yin ibada.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun badda kama sun sace bayin Allah a jihar Neja da ke yankin Arewacin Najeriya. 'Yan bindigan sun zo sanye da kayan jami'an EFCC.
Gwamnan jihar Kaduna, Malam Uba Sani, ya caccaki 'yan siyasa masu siyasantar sa matsalar rashin tsaro. Ya yi gargadin cewa gwamnatinsa ba za ta lamunci hakan ba.
Karamin ministan ayyuka, Muhammad Bello Goronyo, ya nuna cewa samar da ingantattun hanyoyi zai taimaka wajen magance matsalar rashin tsaro a Najeriya.
Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf za ta kashe N8bn domin shirin ciyarwa a watan Ramadan da muke ciki. Shirye-shrye sun kankama.
Karamin ministan gidaje, Abdullahi Ata, ya caccaki mataimakin gwamnan jihar Kano, kan kalaman da ya yi dangane da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun hallaka jami'an tsaro na 'yan banga a wanni harin kwanton bauna da suka kai musu a cikin dajin Matankari da ke cikin jihar Kebbi.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari